19/04/2026
GOBE MAI KYAU NA MATASAN GARIN UBA, JIHAR ADAMAWA
Cikin ikon Allah da yardarsa, ya bai wa wasu matasa—waɗanda ba ma’aikatan gwamnati ba ne, kuma ba manyan ‘yan kasuwa ba ne—sai dai ƙananan almajirai masu neman na kansu daga wajen Allah, damar taimakawa al’ummar Anguwan Dumde Central.
Sun yi babban aiki na gyaran borehole wanda ya lalace tsawon wata guda. A wannan lokaci, al’ummar unguwar sun sha wahala wajen samun ruwa, har suna zuwa daga Dumde zuwa wajen masallacin Juma’a domin samo ruwan ibada da na yau da kullum.
Waɗannan matasa sun nuna tarbiyya da sadaukarwa, inda s**a bayar da abin da suke da shi domin sauƙaƙa rayuwar al’umma. Duk da cewa su ma suna buƙatar kuɗin, sun fifita buƙatar jama’a a kan tasu, s**a aiwatar da wannan aiki na alkhairi.
Ba wannan kaɗai ba ne, kuma su malamai ne da ke karantar da yara a garin, suna ƙoƙarin gina matasa nagari masu tarbiyya.
Hakika, irin waɗannan matasa sun cancanci yabo, addu’a da jinjina daga al’umma. Irinsu ne muke fata Allah Ya ba su damar jagorantar al’umma domin su ci gaba da ayyukan alkhairi.
Suna da ƙungiya ta musamman mai kula da taimakon marayu, marasa ƙarfi, da mabukata gwargwadon iko, ƙarƙashin jagorancin Imam Aliyu Ndotti, wato Qafilatul Mahabbah Islamic Foundation.
Muna roƙon Allah Ya taimaka musu, Ya azurta su da dukiya mai albarka, Ya ƙara musu kishin gari da al’umma.
Ameen summa Ameen.