Ahibba'ul UMMAH

Ahibba'ul UMMAH etc

Ahibba'ul ummah kungiya ce da wasu matasa s**a assasa ta acikin N.D.C ba don komai ba sai dan taimakon addinin musulunci ta hanyar taimakon marayu, ciyarwa lokacin azumi ziyartan marasu lafiya.

02/08/2020

SAQON GODIYA wannan qungiya me albarka qar qashin jagorancin mlm Ahmad Muhammad, ta na miqa saqon godiya da kuma ban gajiya, ga wadanda s**a bada gudunmuwan fatun layyansu, allah ya saka musu da alkhairi, ya sanya musu ladan a mizani. Kadan daga cikin ayyukan wannan qungiya sune kamar haka, taimakon gajiyayyu da marasa qarfi, biyan ma wasu daga cikin marayi kudin makaranta tare da kayan karatu, sannan da ziyartar marasa lafiya a gidajensu da kuma asibitoci. Allah ya saka ma kowa da alkhairi, Rubutawa: ibrahim isah

26/01/2020

AHIBBA'UL UMMAH
N. D. C U/kaji Kaduna

SAKON TA'AZIYYA!!!

Kungiyar AHIBBA'UL UMMAH a madadin shugabanta *malan* *Ahmad Muhammad* na mika sakon ta'aziyya ga *malan* *Bello ( ya* *mu'allim)* da daukacin al'ummar musulmi bisa rashi na mahaifiya da mukayi.

Allah ya jikanta Allah ya gafarta Mata, Allah ya kyautata makwancinta,

*Yahaya Isah*
*AHIBBA'UL UMMAH*
*Social media*
*26/01/2019.*

11/01/2020

*AHIBBA'UL UMMAH!!!* *AHIBBA'UL UMMAH!!!*
*AHIBBA'UL UMMAH!!!*

AHIBBA'UL UMMAH ASSOCIATION,
MOTTO: ISLAMIC CHARITY & DEVELOPMENT ORGANIZATION,*
N.D.C U/KAJI TUDUN WADAN RIGACHIKUN KADUNA.

AIKI GA MAI KARE KA

ZIYARAN KUNGIYAR AHIBBA'UL UMMAH KARO NA FARKO .

A ranar goma ga watan janairun shekara ta dubu biyu da ashirin ne kungiyar AHIBBA'UL UMMAH karkashin jagorancin shugabanta MAL. Ahmad Muhammad. s**a kaddamar da ziyara ta musamman zuwa ga malamai da shuwagabannin unguwa.

A karon farko kungiyar ta samu ziyartar mutane biyu, inda aka gabatar musu da kungiyar tare da kudurorin ta da aikace aikacen ta kasantuwar kungiyar ta samu lokaci mai tsawo tana gudanar da aikace aikacen ta, hakan yaja hankalin shugabanta ya kaddamar da ziyara ta musamman zuwa ga malamai da shugabannin unguwar domin a kara musu sani game da kungiyar, dukka a matakin ci gaba.

*Mutun na farko da kungiyar takai ma ziyara shine, Malan. Abdullahi Ibrahim limamin babban masallacin juma'a na Abubukar siddiq,

*Mutun na biyu kuwa shine Sarkin U/kaji Alhaji Sade Mamman zango

Alhamdulillah , masu iya magana s**ace, " Abinda babba ya hango, yaro ko ya hau tsauni ba ze hango ba " Shawarwari masu fa'idah, lallai kwalliya ta biya kudin sabulu, Allah y ya kaimu ziyara karo na biyu.

*Yahaya Isah*
*Ahibba'ul Ummah*
*Social media*
*11/01/2020**

27/10/2019

Assalamu alaikum warahmatullah wannan qungiya me albarka qarqashin jagorancin malm Ahmad muhammad,tana ma daukacin musulmai na duniya fatan alheri da zama lfya aduk inda suke

29/09/2019

*SAƘON TA'AZIYYA !!!*

_AHIBBA'UL_ _UMMAH (A.U)_

A MADADIN SHUGABAN WANNAN ƘUNGIYA *ML. AHMAD MUHAMMAD*
TARE DA ƊAUKACIN MAMBOBINTA NA MIƘA SAƘON TA'AZIYYARTA GA IYALAN MALAN ANGO, DA AL'UMMAR *N.D.C* TARE DA ƊAUKACIN AL'UMMAR MUSULMI BAKI ƊAYA BISA RASHI DA SUKAYI NA DAN UWA *BABA ADAMU* ,MUNA ROKON ALLAH YAYI MASA RAHAMA ALLAH YA HASKAKA ƘABARINSA ALLAH YASA ƘARSHEN WAHALAR KENAN ALLAH YA MASA SAKAMAKO DA GIDAN AL'JANNAH.

SU KUMA IYALAI, ƳAN UWA DA ABOKAN ARZIƘI ALLAH YA BASU HAƘURIN RASHI.

*AHIBBA'UL UMMAH* *SOCIAL MEDIA.*
*29/01/1440 AH.*
*29/09/2019 CE.*

10/09/2019

Wannan qungiya me albarka tana ma daukacin musulmai na duniya fatan alkhairi, Allah ya biya ma kowa buqatun sa na alkhairi, na sharri kuma Allah ya rabamu dashi

05/09/2019
24/08/2019

Allha ya kara ma members na wannan kungiya me albarka, qwarin gwiwa da jajircewa akan ayyukansu na alkhairi da kuma ci gaba me anfani.

Address

N. D. C Unguwar Kaji Tudun Wadan Rigachikum
Rigachikun
800102

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ahibba'ul UMMAH posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share