02/04/2025
KTSHB
KATSINA LOCAL GOVERNMENT DIVISION
RANA TA FARKO (1): WA'AZIN GORON SALLAH.
A yau Talata 3 ga watan Shawwal Hijrah daga makka zuwa madina shekara 1446 dai dai da 1 ga watan Aprilu Miladiyya Haihuwar Annabi Isah (A.S) shekara ta 2025 Hukumar Hisbah ta karamar hukumar katsina a karkashin jagorancin malam shamsu kabir ta gabatar da wa'azin goron sallah rana ta farko a babban masallacin Juma'ah na garin shinkafi katsina.
A inda Sheik Malam Zainu Abubakar ya gabatar da wa'azi da kuma Shugaban Hukumar hisbah na karamar hukumar katsina malam shamsu kabir ya gabatar da ta'aliqi akan wa'azin, wanda yayi gabatar kuma malam Muhammad Isah Sardauna.
Maudu'in wa'azin shine: Tarbiyya da kuma Muhimmancin ta a
Musulunci.
Wa'azin yayi magana akan:
1. Ma'anar Tarbiyya
2. Yaya ake bada Tarbiyya
3. Minene Hukuncin Tarbiyya a Musulunci.
4. Sharuddan cikar tarbiyya.
5. Muhimmancin Tarbiyya a Musulunci.
Daga karshe Babban Limamin Masallaci Sheik Ibrahim Idris ya rufe taron da addu'a.
Reported by:
Sardauna ICT Unit Hisbah Board KTLG