مركز خالد بن وليد كشنه Cibiyar Khalid bin Waleed Katsina

  • Home
  • Nigeria
  • Katsina
  • مركز خالد بن وليد كشنه Cibiyar Khalid bin Waleed Katsina

مركز خالد بن وليد كشنه Cibiyar Khalid bin Waleed Katsina Son samun tantagaryar gaskiyar labarai da rahotanni.��

YADDA SALAF KE KULA DA MATANSUDaga shafin Dr. Kabir AsgarAl-Imam Azzahabiy (RahimahulLah) ya naƙalto labarin Kulthum Ɗiy...
10/07/2023

YADDA SALAF KE KULA DA MATANSU

Daga shafin Dr. Kabir Asgar

Al-Imam Azzahabiy (RahimahulLah) ya naƙalto labarin Kulthum Ɗiyar Abubakar (RA). Kulthum ta ce: "Na kasance ina addu'a ina cewa: Ya Allah! Ka ba ni miji nagari mai kula da addini, kuma wanda zai lulluɓe ni da soyayya"

Da Allah ya tashi karɓan addu'arta sai a azurta ta da Ɗalhat Ɗan Ubaidullahi (Ɗaya daga cikin mutanen nan goma da aka wa bushara da aljanna).

Kulthum tana ba da labarin irin yadda mijinta ke ji da ita sai ta ce:

"Ɗalhatu ya kasance idan ya kalle ni sai ya yi hailala.

In ya jiyo muryata sai ya yi murmishi

In na fashe da kuka, shima sai ya fashe da kuka

Ba ya yin barci sai ya tabbatar da cewa an gyara min gadona

In ya idar da sallah ba ya yi ma kansa addu'a sai ya fara da ni

In ba ni da lafiya, yakan shiga cikin damuwa, kai ka ce zafin ciwon a jikinsa yake

Ba shi da kwanciyar hankali sai ya ganni zaune a kusa da shi

In muna cin abinci yakan riga ni kai loma bakina

Na kasance abin alfaharinsa a ɓoye da sarari"

DAURAH DAURAH DAURAH Assalamu alaikumAna sanarwa da gayyatar daliban ilimi zuwa wurin DAURAH ta littafin *AL-BULBUL*  na...
24/12/2022

DAURAH DAURAH DAURAH

Assalamu alaikum
Ana sanarwa da gayyatar daliban ilimi zuwa wurin DAURAH ta littafin *AL-BULBUL* na Usulul Fiqhi Wadda zata kasance Kamar haka:
Mai Gabatarwa: *Sheikh Murtala Sani Kerau*
Rana: Laraba 28/12/2022
Lokaci: bayan Sallar Magriba zuwa qarfe 09:00pm na dare
Wuri: Masallacin Talba Ibrahim Kofar Marusa Katsina

Kudin Rajista N200

Domin Karin bayani:
08033352242

Allah ya bada ikon halarta ameen

Assalamu alaikum Ana gayyatar yan uwa zuwa wurin wa'azin WALIMAR auren Ahmad Sulaiman Rahma Wanda za'a yi kamar haka:Ran...
24/05/2022

Assalamu alaikum
Ana gayyatar yan uwa zuwa wurin wa'azin WALIMAR auren Ahmad Sulaiman Rahma Wanda za'a yi kamar haka:
Rana: Alhamis 26/05/2022
Lokaci: Bayan Sallar Isha'i
Wuri: Masallacin Talba Ibrahim Kofar Marusa Katsina
Malami: Sheikh Abdurrahim Sabiu Rafindadi

Domin tuntuba:
08139236136
07035461800

Allah ya bada ikon halarta ameen

20/03/2022

مركز خالد بن وليد كشنه
CIBIYAR KHALID BIN WALEED KASINA

Daurah! Daurah!! Daurah!!!

Wannan cibiya mai albarka na farin cikin sanarwa da kuma gayyatar daliban ilimi zuwa Daurah da aka shirya ta kwana 10 a cikin littafin RA'IYYATUL I'IRAB رائية الإعراب
Wadda zata gudana kamar haka:
Ranaku: 1-10 ga watan Ramadan 1443
Lokaci: 10:00am zuwa 12:00pm
Wuri: Masjid Talba Ibrahim dake cikin makaratar primary ta Talba Ibrahim Kofar marusa Katsina

Mai bukata sai yaje harabar masallacin domin yin registration ko kuma a tuntubi wannan lamba domin karin bayani
08033352242

Ahmad Balarabe Maidole

MARKAZU KHALID BIN WALID KATSINASANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!Wannan Cibiyar dake da headquarter a masallacin Talba Ibrah...
26/02/2022

MARKAZU KHALID BIN WALID KATSINA

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

Wannan Cibiyar dake da headquarter a masallacin Talba Ibrahim dake ƙofar Marusa a cikin garin katsina suna farin cikin gayyatar ku zuwa gagarumin wa'azi na walimar Auren ɗaya daga cikin membobin ta, watau Usman Umar.

Wanda za'ayi kamar haka;

Rana: Asabar 26-7-2022
Wuri: Masallacin Talba Ibrahim a cikin k/Marusa primary school
Lokaci: Bayan sallar magriba
Mai gabatarwa: Dr Muhammad Usamatu Abbas

Allah ya bada ikon Halarta. Ameeen.

17/02/2022

مؤسسة الشيخ محمد ناصر الدين الألباني
Sheikh Muhammad Nasiruddeen El-albani foundation

"Makon Iyalan gidan Manzon Allah (SAW)"

Wannan cibiya mai suna a sama tana gayyatar daukacin Al'ummar Musulmi zuwa wurin karatuka da ta shirya zata gabatar kamar haka:

RANA TA FARKO:
Jumu'a, 17 ga watan Rajab, 1443 AH, dai dai da 18 ga watan February, 2022

Maudhu'i: Iyalan gidan Manzon Allah SAW a Alqur'ani mai girma.

Malami: Dr Mukhtar Usman Jibia
Mai Ta'aliki: Dr Aminu Usman (Abu Ammar)
Mai gabatarwa: Alkali Bunyamin Muhammad Balarabe
Lokaci: Bayan sallar magriba
Wuri: Masallachin jumu'a na Abubakar As-siddeeq, filin samji katsina.

RANA TA BIYU:
Asabar, 18 ga watan Rajab, 1443AH, dai dai da 19 ga watan February, 2022.

Maudhu'i: Iyalan gidan Manzon Allah SAW a Hadith.

Malami: Dr Muhammad Sani Sulaiman
Ta'aliki: Malam Abdullahi Ayyub
Gabatarwa: Malam Munir Isa Kerau
Lokaci Bayan sallar magriba
Wuri: Masallachin Kerau, Katsina.

RANA TA UKKU:
Lahadi, 19 ga watan Rajab, 1443 AH, dai dai da 20 ga watan February, 2022.

Maudhu'i: Hakkokin iyalan gidan Manzon Allah SAW a kan kowane Musulmi, da Hukunce hukuncen da s**a kebance Su.

Malami: Dr Muhammad Usamatu Abbas
Ta'aliki: Malam Abdurrahim Sabi'u Rafin dadi
Gabatarwa: Malam Shamsuddeen Abdulkarim Radda.
Lokaci: Bayan sallar magriba
Wuri: Masallachin Government Printing, kofar Durbi, Katsina.

RANA TA HUDU:
Litinin, 20 ga watan Rajab, 1443 AH, dai dai da 21 ha watan February, 2022.

Maudhu'i: Alaka tsakanin iyalan gidan Manzon Allah SAW da Sahabbai.

Malami: Malam Haruna Muhammad Sani.
Ta'aliki: Malam Safiyyu Alqasim Saulawa
Gabatarwa: Malam Abubakar Mai Kano
Lokaci: Bayan sallar magriba
Wuri: Masallachin Jumu'a na kofar kaura (Kandahar).

CIBIYAR KHALID BIN ALWALEED KATSINAAssalamu alaikunMuna farin cikin sanarwa da kuma gayyatar sugabanni da mambobi na wan...
06/02/2022

CIBIYAR KHALID BIN ALWALEED KATSINA

Assalamu alaikun
Muna farin cikin sanarwa da kuma gayyatar sugabanni da mambobi na wannan cibiya mai albarka Zuwa babban meeting (general meeting) don tattaunawa kan wasu muhimman abubuwa
Taron zai gudana in Allah ya yarda kamar haka:
Rana: Alhamis 10/02/2022
Lokaci: 4:30
Wuri: Hedikwatar cibiyar dake Masallacin Juma'a na Talba Ibrahim Kofar Marusa Katsina

Don Allah wanda ya sani ya sanar da wanda bai sani ba don zuwan kowa yanada muhimmanci.

Allah ya bada ikon halarta

Sanarwa:
Ahmad Surajo Mahmud
08033352242

09/01/2022

MU TARU A MAJALISINSU KAFIN JANA'IZARSU

Alkali Iyadh rahimahullah yake cewa: A lokacin da Muhammad bn Umar bn Lubabah ya cika mutane sun yi goggoriyo aka samu cinkoso maigirma a wurin jana'izarsa sai mahaifinsa Umar ya ce: "Ina ma sun yi irin wannan goggoriyo wajen neman iliminsa kafin jana'izarsa".
📗 Tarteeb al-Madárik (5/157)

07/01/2022

Bayan tsawon lokaci da ya kai kimanin wata shida (6) bai yi limanci a Masalkacin Haramain Sharifain ba Shehun Malami Prof. Sa'ud Shuraim ya ja sallahr asuba ta ranar Lahadin da ta gabata 24-01-2021
Allah ya ƙara masa lafiya da nisan kwana

Tantagarya TV

Hakika duniyar sunna mun yi babban rashi, Allah Ka cike mana wannan gibi da muka samu kanmu a ciki.Ya Allah mun shaida i...
07/01/2022

Hakika duniyar sunna mun yi babban rashi, Allah Ka cike mana wannan gibi da muka samu kanmu a ciki.
Ya Allah mun shaida irin gudunmawarsa ga sunna, Ya Allah Ka sada shi da rahamarka, Ka shada shi da Annabawanka, da shahidai da salihan bayi.
اللهم تقبل منه جهوده العلمية والدعوية.
نشهد له يا ربنا بذلك

Asakamakon zaman da shugabanni da manyan maluma na qungiyar Jamatu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta qasa s...
07/01/2022

Asakamakon zaman da shugabanni da manyan maluma na qungiyar Jamatu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah (JIBWIS) ta qasa s**a gabatar a ofishin shugaban qungiyar na qasa Sheikh Abdullahi Bala Lau tare da shugaban malaman qungiyar ta qasa, Dr. Ibrahim Jalo a sakateriyar qunyar ta qasa anan Abuja, ranar Laraba 5/01/2022.

Qungiyar ta fidda matsaya kamar haka:

i Qungiyar ta bukaci Dr. Jalo da ya dakatar da tattauna wannan matsala ko rubutu akanta a shafin yanar gizo domin wannan matsala, lamari ne da ya shafi maluma da daliban ilimi. Kawota cikin al’umma ba zai haifar da komi ba sai rudani da rashin fahimta;

ii Qungiya ta ja hankalin dukkan maluman da ke qarqashin ta da cewa kafin su kawo wata baquwar matsala ta addani ko fatawa, da su fara gabatar da ita a gaban majalisa don tattaunawa a ilmance da samu matsaya kafin yadata cikin al’umma don kaucewa haddasa rudani da rashin fahimta;

iii Qungiyar tayi kira ga dukkan yan social media da ke qarqashin ta da su dakatar da yada wannan matsala a social media, kuma su janye ta daga shafukan su;

iv Qungiyar tayi kira ga al’ummar qasa da su mayar da hankalin su wajen addu’oin neman zaman lafiya da tsaro, wanda shi ne babban lamarin da yadami wannan qasa a yau;

v Daga qarshe muna addu’a Allah ya qara mana son Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam (SAW) Ya kuma hadamana kan maluman mu bisa Qur’ani da sunnah.

JIBWIS NIGERIA

QISSOSHI 100 DAGA RAYUWAR ABUBAKAR  (R.A)  Na (Sheikh Muhammad Siddiq Alminshawiy)001 ABUBAKAR A TAKAICE (1)Shine Abdull...
03/01/2022

QISSOSHI 100 DAGA RAYUWAR ABUBAKAR (R.A)
Na (Sheikh Muhammad Siddiq Alminshawiy)

001 ABUBAKAR A TAKAICE (1)
Shine Abdullahi dan Usman dan Amir Baquraishe... Abubakar dan Abu-Quhafah Mutumin Taym, Na farko cikin Khalifofi shiryayyu, kuma daya daga cikin mutum 10 da akayi ma bushara da aljanna... Yana daga cikin marigaya na farko... Farkon wanda ya amshi musulunci cikin maza... Kuma ya bada rayuwar shi da dukiyar shi don ciyar da addini gaba... Kuma ya bada kariya ga manzon Allah S.A.W kariya irin ta jarumi gwarzon sadaukiAllah ya bada kariya a hannun shi ga addini da miqaqqiyar hanya... Kuma ya azurta shi da imani da yaqini... Shi tuta (jigo) ne daga tutocin musulmai... kuma takobi ne akan wuyan munafukai da masu ridda

27/05/1443
01/01/2022
✍Ahmad Balarabe Mahmud (Ibn Sira)
08033352242

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when مركز خالد بن وليد كشنه Cibiyar Khalid bin Waleed Katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to مركز خالد بن وليد كشنه Cibiyar Khalid bin Waleed Katsina:

Share