23/05/2026
🌸 Kyawawan Ɗabi’un Manzon Allah (ﷺ) 🌸
Daga Anas Ɗan Málik (R) ya ce: ((Ya wuce ta kusa da wasu yara ƙanana sai ya yi musu Sallama, sannan ya ce: Manzon Allah (ﷺ) ya kasance yana yin hakan))
📚 Sahihul Bukhári.
✨ Wannan yana nuna irin tawali’u da rahamar Manzon Allah (ﷺ). Duk da matsayinsa, yana kula da yara yana gaishe su cikin fara’a da ƙauna.
🤝 Mu ma mu koya yin sallama da fara’a ga manya da yara, domin sallama tana ƙara soyayya da haɗin kai a tsakanin Musulmi.