08/04/2025
Ka tsaya a inda kake ka bautawa Allah a gurin.
Daga Abu Sa'ed Allah ya yarda dashi, wani mutumin karkara yazo gurin Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya tambayeshi game da hijra ( Yana so ya baro kauyensu ya dawo gurin Annabi) Sai Annabi yace masa, ahir dinka, sha'anin hijrah Yana da tsanani ( nauye nauyenta da hukunce hukunce) Amma ka na da rakuma? Mutumin yace: Eh, Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yace: kuma kana bayar da zakkarsu? Mutumin yace : Eh, Sai Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yace: acikinsa akwai wacce kake bayarwa (ga mabukata) su tatsi madararta? Mutumin yace: Eh, sai Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) Yace: Kuma kana tatsar madarar idan anje bawa rakuman ruwa? Mutumin yace Eh, sai Annabi (sallallahu alaihi wa sallam) yace: ka yi aikinka (na da'a) a kauyen, Don Allah ba zai tauye Maka komai cikin ayyukanka ba.
Bukhari da muslim
جَاءَ أعْرَابِيٌّ إلى النَّبيِّ صلَّى اللهُ عليه وسلَّمَ، فَسَأَلَهُ عَنِ الهِجْرَةِ، فَقالَ: ويْحَكَ! إنَّ الهِجْرَةَ شَأْنُهَا شَدِيدٌ، فَهلْ لكَ مِن إبِلٍ؟ قالَ: نَعَمْ، قالَ: فَتُعْطِي صَدَقَتَهَا؟ قالَ: نَعَمْ، قالَ: فَهلْ تَمْنَحُ منها شيئًا؟ قالَ: نَعَمْ، قالَ: فَتَحْلُبُهَا يَومَ وِرْدِهَا؟ قالَ: نَعَمْ، قالَ: فَاعْمَلْ مِن ورَاءِ البِحَارِ؛ فإنَّ اللَّهَ لَنْ يَتِرَكَ مِن عَمَلِكَ شيئًا.
أخرجه البخاري كتاب مناقب الأنصار ب هجرة النبي صلى الله عليه وسلم وأصحابه إلى المدينة 2/257 الحديث 3923 وفي الزكاة ب زكاة الإبل عن على بن عبد الله.
وأخرجه في كتاب الأدب ب ما جاء في قول الرجل ويلك 3/170 الحديث 6165 عن سليمان بن عبد الرحمن.
وأخرجه مسلم كتاب الجهاد والسير ب المبايعة بعد فتح مكة..... 7/8 الحديث 1865 (مع المنهاج) عن أبي بكر بن خلاد الباهلي
ثلاثتهم ( على بن عبدالله وسليمان والباهلي) عن الوليد بن مسلم.
وأخرجه البخاري كتاب الهبة وفضلها ب فضل المنيحة 2/24 الحديث 2633 ومسلم 1865 عن الدارمي كلاهما ( البخاري الدارمي) عن محمد بن يوسف.
كلاهما ( الوليد بن مسلم و محمد بن يوسف) عن الأوزاعي عن الزهري عن عطاء بن يزيد عن أبي سعيد الخدري رضي الله عنه به.
Hamza Diso