Muassasatu Shaik Muhammad Khamis Alkhairiyyah HQ Kofar Kabuga Kano State.

  • Home
  • Nigeria
  • Kano
  • Muassasatu Shaik Muhammad Khamis Alkhairiyyah HQ Kofar Kabuga Kano State.

Muassasatu Shaik Muhammad Khamis Alkhairiyyah HQ Kofar Kabuga Kano State. Wannan Shafi yana dauke ne da bayanai tare da fadakarwa da waazantar da wannan kungiya take yi ga Al

Gayyatar Mauludi!!!Sheik Abulkadir Mai Anwaru ya na gaiyatar yanuwa Masoya Fiyayyen Halitta zuwa wajen Taron maulidin sh...
09/02/2024

Gayyatar Mauludi!!!

Sheik Abulkadir Mai Anwaru ya na gaiyatar yanuwa Masoya Fiyayyen Halitta zuwa wajen Taron maulidin shugaba SAW Wanda ya sabawa gatarwa duk Shekara Wanda zaayi ranar lahadi 11/2/2024 daidai da 30/Rajab/1445 da karfe 8:00 na dare zuwa Abinda ya sauwaka, a Jamiul Anwar Dake unguwar tudun Yola gate 5 gwale LG Kano.

Allah ya bada ikon Zuwa Ameen.

SANARWAR RASUWAR MAHAIFIYAR MARIGAYI MAL NASIR KHAMIS MAISUNAN MALAM KABUGA, ALAL MISALI AYAGILIMANMIN TURASUL ISLAM GOR...
14/10/2023

SANARWAR RASUWAR MAHAIFIYAR
MARIGAYI MAL NASIR KHAMIS MAISUNAN MALAM KABUGA,
ALAL MISALI AYAGI
LIMANMIN TURASUL ISLAM GORON DUTSE

```انا لله وانا اليه راجعون ان لله ما أخذ وله ما أعطى وكل شيء عنده بمقدار

Allah ya yiwa Hajiyan Dorawa Rasuwa
Mahaifiya Ga Marigayi Mal. Nasir Maisuna Mallam Mallam Da Mal. Mujitafa Limamin Turasu.

Ta rasu Asafiyar yau Asabar 14/09/2023 a Garin Dorawan Babuje da ke Barikin Ladi (LGA) Jos Plateau State.

Za ayi Jana'izarta a can garin Dorawan Babuje da karfe 2:00pm na Rana.

Muna fatan za a saka ta acikin Addu'o'in ku.
Saboda da nisa ga lambar khalifofin don yi musu ta'aziyya.

1.Liman Mal. Mujtaba Khamis 07030284728

2, Khalipa Mal Bashir Dorawa Jos 08153323298

3. Mu'ayyad Nasir 'Da ga Maisunan Malam 07061239433

Allah ya jikanta da rahama ya gafarta mata ya bamu hakurin rashinta Ameen.

Sanarwa
Muasssasatu Sheikh Khamis Alkhairiyya kano
08038428244

30/07/2023
Gayyatar Daurin Aure!!!Iyalan Marigayi Alhaji Zakari                      Muhammad AyagiDana Marigayi Alhaji Lawan Maitu...
24/07/2023

Gayyatar Daurin Aure!!!

Iyalan Marigayi Alhaji Zakari Muhammad Ayagi
Dana
Marigayi Alhaji Lawan Maiturare

Suna Farin cikin gayyatar Al'umma Zuwa Wajen Daurin Auren Yayan su

Imam Sani Zakariyya
(Limamin Masallacin Juma'a na Ibadurahman Tudun Yola)
Da
Husaina Lawan Maiturare

Wanda Za'a yi insha Allahu k**ar haka :

Rana: Juma'a 28/7/2023 = 10/01/1445
Lokaci : 10:00 na safe
Wuri : Masallacin Alhaji Lawan Maiturare dake Kofar Kabuga, Daura da Tudun yola Gate 1 Layin Hajiya Yabi Makarantar Kowanaso, Jihar Kano.

A iso lafiya

08038428244
09069067433

18/06/2023

FALALAR GOMAN FARKON ZUL-HIJJA
Daga Auwal Zakari Ayagi
Chairman Alazmiyyah Islamic Foundation Kano

Da sunan Allah mai yawan Rahama, Mai yawan jin kai, tsira da Aminci su kara tabbata ga fiyayyan halitta Annabin rahama, tare da saabbansa da iyalan gidansa, da duk masu binsa da kyautatawa har zuwa ranar Alkiyama.

Bayan haka sabo da ganin kusantowar watan da yake kunshe da manya manyan falaloli, da darajoji a kwanaki goma na farkonsa wato kwanaki Goman farkon watal zul hijja, naga yadace in dan dada tinatar da yanuwa almajirai mahimmanci, tare da girman da Allah ya yiwa ranakun, tare da irin abubuwan da ya dace mu aikata a ranakun don kara neman kusanci da Allah Subhanahu Wataala.
Dafan Allah ya amfanar damu, abin da aka gain na kuskure Allah ya yafe.

WADANNENE RANAKUN FARKON ZUL HIJJA
Ubangiji madaukakin sarki yana fada cikin alkur,ani mai girma cikin suratul fajar aya ta 1-3 "INA RANSTUWA DA ALFIJIR, DA RANAKU GOMA, DA SHAF,I DA WUTIRI" Manyan malamai sunyi maganganu masu yawa akan wadannan ayoyi, amma Abdullahi ibn Abbas Allah ya kara yarda agareshi yace; Abin da Allah yake nufi da Alfijir shine sallar Asubahi, Darare goma kuwa sune goman zulhijjah, shafa,i kuma shine halitta, Wutiri kuma shine Allah. Allah ya ambace su sune darare goma, domin ranaku ne Tara da dare goma, saboda girman da wadannan ranaku suke da shi har Allah {SWT} yayi ranstuwa dasu cikin littattafansa mai girma.

DAUKAKA DA DARAJOJIN RANAKU GOMA NA ZULHIJJA
Waddannan ranaku suna da matukar girma da daukaka domin an karbo Hadisi daga dan Abbas Allah ya kara yarda a gareshi, cewa shi ya ce Acikin goman farko na zulhajji Allah ya karbi tuban Annabi Adam (A.S). Cikinsa ne Annabi Ibrahim ya gina Kaaba, acikinsune Allah yayi munajati da Annabi Musa, harila yau acki aka saukarwa da Annabi Dawud gafara, aciki ranar Tarwiyya take, da ranar Arfat, da ranar layya, da kuma ranar Hajji.

An karbo daga Abi Said Alhudri (RTA) daga Manzon Allah (SAW) yace; “Suhgaban watanni watan Ramadan, mafi girmansu kuma Zulhijja.

FALALAR WATAN ZULHIJJA
An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda agareshi, daga Manzon Allah Salallahu Alaihi Wasallam yace; Mafifitan Ranakun duniya Ranaku na Zuihijja. Ankarbo daga Addau dan Rabia yace; Naji Sayyada Aisha (RTA) tace; Yakasance lokacin Annbi (SAW) wani mutum ya kasance idan watan Zulhijja ya k**a sai ya wayi gari yana Azumi sai wannan labari ya riski Manzon Allah (SAW), Sai aka zowa Annabi Alaihissalam da shi, sai yace dashi meyasa kake Azumtar wadannan ranaku? sai yace ya Maaikin Allah sun kasance ranakune na haduwa, kuma ranaku ne na aikin hajji, sai nake so ubangiji ya hadani a cikin Adduoin da ake yi a ciki, sai Annabi Alaihissalam yace da shi, ya tabbata ageka ko wacce rana da kai Azumi k**ar kayanta wuyaye dari ne, kayi hadaya da taguwa dai, ka bayar da dawakai dari don daukaka Addinin Allah, amma kuma in ka Azumci ranar Arfa k**ar ka yenta wuyaye dubu biyu ne, kayi hadaya da taguwa dubu biyu, ka bayar da dawakai dubu biyu don Allah, kuma k**ar ka Azumci shekarar da ta gabata ne da kuma shekara ta gaba.

Buhari da Muslim sn rawaito hadisi cewa Manzon Allah Alaihissalam yace; Babu wadansu ranaku da Allah Yafi son Alheri a cikinsu fiye da wadannan ranaku, ina nufin ranakun fakon Zulhijja, sai akace ya ma'aikin Allah ko jihadi ne? sai yace ko da jihadi ne, sai dai mutumin daya fita da kansa da dukiyarsa, sannan bai dawo da komai ba.

FALALAR AZUMTAR RANAR ARFA
Muslim ya rawaito cewa Manzon Allah Alaihissalam yace: "Azmin ranar Arfa yana kankare zunuban shekaru biyu da s**a gabata da shekara ta gaba." An rawaito daga sashin matan Manzon Allah cewa; Manzo Alaihissalam ya kasance yana azumtar tara na zulhijja (Abu Dawud)

Azumtar wadannan ranaku yana da matukar mahimmanci k**ar yadda mukaji daga bakin shugaba Alaihissalam musamman ranar Tara ga Zulhijja wato ranar ARFA k**ar yanda yazo a hadisin Buhari da muslim daya gabata.

AIKATA AYYUKAN ALHERI
Haka zalika anaso a yawaita sauran ayyukan alheri, domin Allah ya matukar son ayyukan alheri a ranakun, k**ar yawaita tasbihi, da salatin Annabi, sada zumunci, yawaita nafil fili, da istigifari, da karatun Alkurani, kyautatawa iyali, ziyarar marasa lafiya, farantawa iyaye, da kara biyayya agaresu , tufatar da muminai da ciyar dasu ko shayar dasu, musamman masu tsananin bukata, jinkan marayu, musamman shafa kansu da kyautata musu, da sauran ayyukan alhei, amma ubangiji yafi son a yawaita kabarbari a wadannan ranaku musamman a salloli goma sha biyar, daga sallar Azahar taranar zuwa sallar Asubahi ta ranar uku ga sallah, domin Abdullah Ibn Abbas ya kasance yana bin kasuwa yana kabarbari don tunawa mutane kada su shagala.

SALLAR IDI BABBA
Sallar idi Babba Sunnace mai karfi. Ubangiji Mai Girma da daukaka ya umarni da yinta cikin Littafinsa Mai Girma in da ya ke cewa: Hakika mun baka Alkausara, kayi Sallah ga Ubangijin ka, ka soke abin yankanka (Suratul Kausar aya ta 1-2).

Manzon Allah Alaihissalam ya yita kuma yayi umarni da yinta, ya fita don yin Sallar tare da Mata da Yara kanana, Sallar tana kara Imani da tsoron Allah. Ana yin tane a ranar Goma ga Zulhijja.

LOKACIN SALLATARTA: Lokacin da ake Sallatar Idi babba shine daga lokacin da Rana ta d**o, ana so a yita dawuri domin Mutane su samu suyi layya da wuri, k**ar yadda Shugaba (SAW) ya aikata.

LADABAN SALLAR IDI: Ladaban Salla sune k**ar haka:

1. Wanka da sanya sababbin tufafi ko mafiya kyau, tare da fesa turare, saboda fadin Annabi Alaihissalam cewa: Manzon Allah ya umarcemu a ranakun idi biyu da musanya tufafi kyawawa, mu fesa turare mafi kamshi.,(Hakim)

2. Yana daga Ladaban ta kame baki har sai an dawo daga Masallaci, k**ar yadda Aba Buharra yafada cewa: Shugaba Alaihissalam ya kasance baya cin Abinci ranar idi Babba har sai yadawo gida sai yaci daga layyarsa (Turmuzi)

3. Yin Kabarbari daga daren Idin har zuwa karshen ayyamul tashreek (wato kwanaki ukun bayan salla), lafazin Kabarbarin shi ne: ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR LAILAHA ILLALLAHU ALLAHU AKBAR ALLAHU AKBAR WALILLAHIL HAMDU. Ana karfafa fadarsu yayin tafiya masallaci.

4. Yana daga Ladabanta canja hanyar da aka tafi yayin dawowa, Saboda Shugaba Alaihissalam ya kasance yana canja hanya a ranar idi (Buhari)

5. Yin Sallah a sarari ma'ana ba a cikin masallaci ba, sai dai idan da lalurar ruwa ko mak**ancin haka, to sai ayi a cikin masallaci.

5. Taya juna farin ciki tare da fadin musulmi ga danuwansa, Allah ya karba agareni ya karba a gareka. Kamar yadda aka rawaito Sahabban Manzo sun kasance idan sun hadu da yan'uwansu suna fadin Allah ya karba garemu da gareka (TAKABBALALLAHU MINNA WA MINKA).

YANDA AKE YIN SALLAR IDI

Yadda ake yin Sallar Idi shine, mutane su fito izuwa masallaci yayin da rana tafito, sai liman ya tsaya don Salla batare da kiran Salla ko ik**a ba, zaiyi Rakaoi biyu, a rakaar farko zai yi kabarbari guda bakwai, tare da kabbarar harama, mutanen da suke bayansa za su rika yin kabbara a duk yayin da yayi kabbararsa, sai ya karanta Fatiha da Suratul Aala, a bayyane. A rakaa ta biyu, zai yi kabarbari guda shida tare da kabbarar tsayuwa, zai karanta Fatiha da suratul Jashiyati ko suratul Shamsi, idan yayi sallama sai ya tashi don yiwa mutane huduba.
Bayan ya budeta da yabo da Allah, da godiya a gareshi, sai ya kwadaitar da mutane akan falalar yin Layya da bayyanamusu hukumce-hukumcenta da yanda a ke yenta da kuma lokacin da ake yita, yayin daya k**ala huduba sai mutane su taya junansu murna, sannan su koma zuwa gidajensu, ba za ayi sallar nafila ba bayan sallar Idi ko kafinta, sai dai in wanda sallar Idin ta kubuce masa ne, sai ya sallaceta rakaa hudu, saboda fadin Ibn Masud Allah ya kara yarda a gareshi: Wanda Sallar Idi ta kubuce masa ya sallaci rakaa hudu, amma wanda yariski wani abu tare da Liman koda zaman tahiya ne to sai ya tashi bayan liman yayi sallama ya sallaci rakaa biyu.

Wadannan sune bayanai game da falalar da take cikin Goman Farko na Zulhijja tare da bayanai game da Sallar Idi babba.

Wassalamu alaikum warahamatullahi taala wa barakatuhu.

Innalillah wa Inna Ilaihir RajiunA yau Marigayi Shaik Nasir Muhammad Khamis Ayagi (MaiSunan Mallam Kabuga) ya cika Sheka...
09/03/2023

Innalillah wa Inna Ilaihir Rajiun

A yau Marigayi Shaik Nasir Muhammad Khamis Ayagi (MaiSunan Mallam Kabuga) ya cika Shekaru biyar da Rasuwa, ya koma ga Allah ne Ranar Juma'a 9/3/2018 bayan gajeriyar jiyya a Gidan sa dake Tudun Yola.

Mal. Nasir Muhammad Khamis kafin rasuwarsa limamin Masallacin Juma'a ne na Turasu ya rasu yabar Mata biyu da iyalai da dama.

Hakika rashin Mallam babban rashi ne a garemu da a kullum muke tinawa da shi, Allah ya jikansa Allah ya gafartamasa Ameen.

06/01/2023

TAAZIYYA! TAAZIYYA!! TAAZIYYA!!!

HUKUMAR ZARTARWA TA MAKARANTAR MAAHAD SHEIKH KHAMIS COLLEGE OF QUR'ANIC STUDIES, KOFAR KABUGA

A madadin Hukumar Zartarwa (Governing Council) na Makarantar Maahad Sheikh Khamis College of Qur'anic Studies, Kofar Kabuga ,da Jagororinta, iyaye da dalibai muna mika sakon Taaziyya ta Shugabanmu Marigayi Alhaji (Dr) Adamu Aliyu Sumaila (Dawakin Sumaila) ,Tsohon Shubagan Karamar Hukumar Sumaila, Tsohon Shugaban Jamiyyar PDP ta Jihar Kano, Tsohon Shugaban Hukumar Gudanarwar Kwalejin Ilimi ta Tarayya( FCE ) Obudu, Jihar Cross River, Tsohon Shugaban Kungiyar Ma'aikatan Lafiya na Jihar Kano, wanda Allah SWT Ya karbe shi jiya Alhamis 5/01/2023.

Allah Ya jikansa da rahama, Ya sanya Aljannatul Firdausi ce masaukinsa. Hidimar da Yayiwa addinin Musulunci , da Makarantunmu ( Tahfizul Quran Islamiyya, Khadijah Islamiyya da Maahad Sheikh Khamis) Allah Ya sanya masa su a Sadakatul Jariyya.

Hakika munyi rashin Shugaba kuma Jagora Masoyin Mallam.

Allah Ya kyautata makwancinsu baki daya, Ya kuma kula da bayansa.

Hakika ba zamu manta gudunmawarsa da ya bayar ga wannan Makaranta ba, tun daga kaddamar da asusun gina ta, izuwa tallafinsa na ginata tun daga aza bulo na farko har zuwa gina ta a yadda take yau. Dukka da aljihunsa, da agajinsa akayi su.

Allah SWT Ya saka masa da Gidan Aljanna, Ya kuma yafe masa kurakuransa.

A madadin Yan Kwamitin Zartarwa, ina kara mika taaziyyarmu ga daukacin iyalai, yanuwa,masoya da sauran alummar Musulmi a bisa wannan babban rashi. Allah SWT Ya bada hakuri da juriya.

Allah Ya sakawa duk wadanda s**a halarci janaizar ko kuma yi masa addua.

Bisalam
*Bala Muhammad Tanko*
(Secretary to the Council)
A MADADIN HUKUMAR ZARTARWA.

04/03/2022

BARKANMU DA JUMMA'A

31/01/2022

SALLU ALA MUHAMMAD

31/12/2021

ALHAMDULILLAH

Address

Head Office Kofar Kabuga Opp. Primary School Kano
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muassasatu Shaik Muhammad Khamis Alkhairiyyah HQ Kofar Kabuga Kano State. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share