22/07/2026
Assalamu Alaikum !
A jiya Talata 21st July, 2026 sakataran wannan kwamiti mai albarka na AL-YATAAMA, kuma na'ibin Liman na II na Masallacin Mus'ab Bn Umair, Kofa, watau Malam Umar Nasir Kofa ya bar gida Nijeriyya domin zuwa ƙasa mai tsarki don gudanar da aikin Umara.
Malam Umar tare da wasu daga cikin mutanan wannan gari mai albarka sun bar gida Nijeriyya a jiya Talata da misalin karfe 11 na safe wanda yanzu haka sun sauka a kasa mai tsarki domin gudanar da ibadah.
Muna addu'ar, Allah ta'ala yasa suyi ibada karbabbiya, ya kuma dawo mana dasu gida lafiya.
Sanarwa: Abdulrazak Aminu Kofa, Publication Chairman, AL-YATAAMA Foundation, Kofa.