AHLIL KISA'I TV

AHLIL KISA'I TV Tasha ta musamman dake Yada harkokin Gidan Annabta daga kowana Bangaren Addini Batare Da Nuna Ban Bancin Aqidaba

Kotu ta bawa Mallam shawara ya dau lauya, kuma yanzu ya gane cewa case din sa sai da lauya.Mallam ya yarda zai dau lauya...
23/04/2026

Kotu ta bawa Mallam shawara ya dau lauya, kuma yanzu ya gane cewa case din sa sai da lauya.

Mallam ya yarda zai dau lauya. Kuma yayi Godiya.

Za a koma kotun Afil ta High Court Kano dan a cigaba da case.

Saboda babu wani Afil da yake gaban ta yanzu, da Mallam da lauyoyin Gwamnati duk basu shigo ta kofa mai kyau ba.

Duba da yanayin case din, saboda adalcin Shari’a.

An maida wannan Afil zuwa gurin Cif joji na kano dan ayi Shari’a cikin Gaggawa.

Kuma a mayar da Mallam gidan gyara Hali.

Wannan shi ne Odar da Kotun Afil ta Bayar.

DAGA NAN KOTU YANZU HAKA
23/04/2026

DAGA NAN KOTU YANZU HAKA

Al Hamdu Lillahi:- Shiekh Abduljabbar Yasami Shiga Cikin Koru Tin Misalin 7:15am  Wane Fata Kikemasa Awan nan Lokaci  ?
23/04/2026

Al Hamdu Lillahi:- Shiekh Abduljabbar Yasami Shiga Cikin Koru Tin Misalin 7:15am Wane Fata Kikemasa Awan nan Lokaci ?

حسبنا الله ونعم الوكيل يا قهار يا جبار 🤲🤲🤲
23/04/2026

حسبنا الله ونعم الوكيل يا قهار يا جبار 🤲🤲🤲

In Sha Allahu Sallar Juma'ar 24/04/2026 Agida Zakayita Cikin iyalanka Bijahi Rasulillahi (s.a.ww)
22/04/2026

In Sha Allahu Sallar Juma'ar 24/04/2026 Agida Zakayita Cikin iyalanka Bijahi Rasulillahi (s.a.ww)

21/04/2026

AMSAR TAMBAYAR PASTOR: Daya Daga Cikin Ɗaliban Shikeh Abduljabbar Kabara Mai suna Malam Lamin Jos ya Amsa Tambayar Da pastor Emmanuel Yayiwa Sarkin Musulmai Da kuma Shiekh Ahmad gumi
21 - 04 - 2026

AL BISHIRINKU: Kotu Tabada Umarnin Adawo Da Malam Abduljabbar Kano. Yazo Yakare Kansa  Ranar Al'hamis..
20/04/2026

AL BISHIRINKU: Kotu Tabada Umarnin Adawo Da Malam Abduljabbar Kano. Yazo Yakare Kansa Ranar Al'hamis..

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Umarnin A Kawo Malam Abduljabbar A Zama Na Gaba Don Halartar Shari’arsaKotun Ɗaukaka Ƙara da ke...
20/04/2026

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Yi Umarnin A Kawo Malam Abduljabbar A Zama Na Gaba Don Halartar Shari’arsa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zaman ta a Sakatariyar Audu Bako a birnin Kano, ta ba da umarnin lallai a gabatar mata da Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara a zama na gaba, bayan malamin ya buƙaci hakan ta hanyar rubuta wasiƙa daga gidan yarin Kuje.

Sheikh Abduljabbar, wanda wata Babbar Kotun Shari’ar Musulunci ta yanke wa hukuncin kisa a baya, ya daukaka kara ne domin kalubalantar hukuncin. Sai dai a zaman na yau, an samu tsaiko sakamakon rashin halartar malamin da kuma rashin zuwan lauyoyin gwamnati.

Duk da cewa Sheikh Abduljabbar bai samu damar halartar zaman na yau ba, wakilinsa, Jilani Ibrahim Makwarari, ya mika wa kotun bukatar malamin ta hanyar wasika.

A zantawarsa da manema labarai, Comr. Bashir Ibrahim Magashi, daya daga cikin wadanda s**a halarci zaman, ya bayyana cewa malamin yana neman kotu ta ba da umarnin dawo da shi Kano daga gidan yarin Kuje na Abuja.

"Malam ya rubuta wasiƙar ne don ya shaida wa kotu cewa tun bayan fitar da shi daga gidan yarin Kurmawa zuwa Kuje, bai san halin da takardunsa na shari'a suke ciki ba. Don haka yake roƙon a dawo da shi domin ya kula da takardunsa sannan ya tsaya wa kansa," in ji Magashi.

A farkon zaman, an samu rashin jin dadi daga bangaren alkalai sakamakon rashin wakilcin lauyoyin gwamnati. Bayan an bayar da umarnin kiran su, alkalai sun nuna bacin ransu kan abin da s**a kira rashin girmama kotu da rashin mutunta tsarin shari'a.

Daga bisani, kotun ta bukaci lallai gwamnati ta samar da lauyan da zai ci gaba da bibiyar shari'ar yadda ya kamata.

Bayan sauraren jawaban da aka gabatar, kotun ta dage sauraren karar zuwa ranar Alhamis, 23 ga watan Afrilu, 2026.

Haka zalika, kotun ta ba da umarnin lallai a gabatar da Sheikh Abduljabbar a ranar domin ya kare kansa kamar yadda doka ta tanadar masa.

16/04/2026

ALLAH YA ISAH: Sabuwar Wakar Malam Bashir Dan D**o Mai Suna Allah Ya isah

11/04/2026

SUWAYE AHLUL-BAITIY: DAGA BAKIN MARIGAYI SHIEKH ALIYU MAI SHARIFIYA WARURE

AHLIL KISA'I TV

Iran Ta Wulakanta Amurka A Pakistan An dasa mana tunanin cewa lallai Amurka ita ce take da mabuɗin duniya a aljihunta. I...
11/04/2026

Iran Ta Wulakanta Amurka A Pakistan

An dasa mana tunanin cewa lallai Amurka ita ce take da mabuɗin duniya a aljihunta.

Iran ta sauya taswirar darajar ɗan adam a yau, 11 ga Afrilu, 2026. J.D. Vance, Mataimakin Shugaban Ƙasar Amurka, ya sauka a Pakistan da nufin tattaunawa, amma abin da ya faru ya girgiza daukacin fadar White House. Iran ta sanya wa Amurka Deadlock, inda ta ƙi fitowa tattaunawar gaba ɗaya a daren yau.

Wani lokacin, shiru shine abinda ya fi ƙarar bom raɗadi. Iran ta nuna wa Donald Trump cewa ita ba Lebanon ba ce, ba Venezuela ba ce, kuma ba Nigeria ko South Africa ba ce, Iran ita ce Iran. Ta sanya sharudda guda biyu kafin ta zauna a teburin shawara: Na ɗaya, dole Isra'ila ta daina kwarara bom a Lebanon yanzu-yanzu. Na biyu, dole Amurka ta saki dukiyar Iran da ta danne (Frozen Assets) kafin a fara magana. Wannan hikima ce ta kwararru; ba zaka je neman maslaha kana roƙon a ba ka abin da yake naka ba. Dole a ba ka naka, sannan a fara maganar wasu.

Babban abin da ya kamata ka tambayi kanka shine: Wa yake cikin matsin lamba a yanzu? Amurka ce take roƙon sulhu don ta sami numfashin gudanar da harkokinta, yayin da Iran take riƙe da igiyar. Trump ya yi sauri ya rattaba hannu akan wasu sharudda 10 don kawai ya sami hutu, amma yanzu yana ƙoƙarin kauce wa alkawuran sa. Iran kuwa ba ta yarda da yaudara. Sun koyi darasi daga baya; ba za su sake yarda a yaudare su ba yayin da ake tsaka da tattaunawa.

Duk da cewa Amurka tana ci gaba da tura makaman yaƙi zuwa Gabas ta Tsakiya, yin hakan ba tsoro ya ba wa Iran ba, illa ƙara tabbatar mata da cewa babu amana a tare da su. Bayan wannan shirin, akwai ƙattai guda biyu dake goyon bayan Iran, China da Russia. China ba ta son ganin an yi wannan sulhun cikin sauƙi, domin tana son duniya ta ga gazawar Amurka a fili. Iran tana wasan kwaikwayon da ya wuce tunanin kowa; tana amfani da Strategic Distrust don shaqe numfashin diflomasiyyar Yamma.

Idan baka zama babban mai nazari (Analyst) ba, zaka zama abincin farfaganda. Gaskiyar magana ita ce Wanda yake da gaskiya, ba ya tsoron tsayuwa akan ƙafafunsa.

Kuyi register da AREWA TOPUP don samun data akan farashin da kukeso

10/04/2026

IRAN BADAN MUSULUNCI TAKE YAKIBA:
Cewar Lawan Turayam Cikin Wani Karatun da yagabatar a shekaranjiya Sai Dai Ya sami Amsar Wasu Magan ganu daga Bakin Wani Mabiyin Mazhabar Shi'a

Address

664 Warure, Sani Buhari Road
Kano
700251

Telephone

+2348020505610

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AHLIL KISA'I TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to AHLIL KISA'I TV:

Share