09/09/2026
Sheikh Musa Ayyuba Lukuwa ya yi karatun wanda ya karanto daga littafan Musulunci. Duk da cewa wasu za su iya cewa usulubinsa bai yi musu ba, amma sun san cewa ba shi ne ya ƙirƙiro karatun ba, akwai shi a rubuce cikin littafan Musulunci.
Maimakon masu ilimi su ƙalubalanci Sheikh Lukuwa, sai wawayen gari saboda jahilcinsu da kuma zuga daga jahilan malamai, sai s**a fara cin alwashin hàlaka Sheikh Lukuwa, kamar yadda babban Tsagera, wato Mai Barewa, ya dinga sakin video episode-episode na zagi da barazana. Alhamdulillah, Ahlussunnah ansha su sun warke. An kàshe Sheikh Albani da Sheikh Ja’afar, don haka sun shirya wa ƙananan marasa kunya. A halin yanzu Mai Barewa na gidan gyaran hali. Wannan salon na ’yan bidi’a ya rushe nan take.
Maimakon waɗannan malamai su karbi tayin muqabalar da Sheikh Lukuwa yaketa aika musu, ko su sa Gwamnati ta shirya musu muqabala domin su titsiye Sheikh Lukuwa, sai s**a kauce wa jin kunya saboda sun ga yadda Mal. Lawan Triumph ya biya wa ’yan bidi’ar Kano karatu dalla-dalla.
Yanzu abin da suke so wai kawai Gwamnati ta ɗauki mataki a kan Sheikh Lukuwa, saboda sun rasa yadda za su yi da shi, ga shi kuma suna tsoron jin kunya idan aka haɗa musu zama da shi.
Tambaya zuwa ga waɗannan ƙungiyoyin Bidi’a kamar haka:
1. Me ya sa ba ku taɓa yin ganganmi domin tilastawa Gwamnati ta hana shirka da bidi’a a hubbarar Shehu ba?
2. Me ya sa duk kashe-kashe da sace-sacen mutane da ake yi a Jihar Sokoto, ba ku taɓa taro a kai ba?
3. Me ya sa kuka ƙi karɓar tayin muƙabalar da Sheikh Lukuwa ya aika muku?
4. Me ya sa ba za ku ce Gwamnati ta shirya muku zama da shi ba, sai dai ku ce Gwamnati ta ɗauki mataki a kansa?
Allah ka raba mu da bidi’a. Amin.