30/04/2026
Sheikh Ibrahim Aliyu Kaduna ya yaba wa Prof. Maqari tare da yi masa addu’a kan samar da jami’ar mata zalla a garin Zaria mai suna Tazkiyah University Kaduna. Sannan ya yi kira ga Malaman Izala da su rigangeniya a irin wannan aikin domin share wa Musulmai hawaye.
Dr. Jamilu ya yi raddi ga Sheikh Ibrahim Kaduna akan wannan yabo da addu’a da ya yi wa Prof. Maqari tare da cewa kome ɗan bidia ya yi ba a yabonsa, domin wannan makaranta ma koyarwa da bautar Annabi da shehunai za a yi koyar. 😂
Sannan ya ce saboda darika ta fara mutuwa aka shigo da wannan yaudara ta jami’ar mata zalla, kana Ahlussunnah ka ɗauki yarka ka kai ta sai a koya mata darika ta haifi ’ya’ya duk su zama ’yan darika.
Abin takaici Dr. Jamilu bai iya isar da sakonsa ba sai da ya furta waɗannan kalmomi cikin vedion da ba fi minti biyar ba, ga su kamar haka;
1. Rubabbun malamai
2. Rashin hangen nesa
3. Mai ƙarancin tunani
4. Mai ƙarancin hangen nesa
5. Kwadayi ya mamaye zuciyarsu ba sa gane fari da baki
6. Kwaram da ci da addinin Malaman Ahlussunnah s**a saka a gaba
7. A ci da addini an ci da addini
Dan Allah wannan sunansa raddi ko cin mutunci? Kuma abin takaici shi ne Dr. Jamilu bai san ma wacce kalar jami’a Prof. Maqari ya samar ba wallahi.
A hoto na sama ga “about” din Tazkiyah University nan, sannan ga take off faculties and programmes da wannan jami’a da za ta gudanar. Dan Allah a ina ne aka ce za a koyar da Diwani, Jawahirul Ma’ani, Salatul Fati, tarihin rayuwar Sheikh Inyass ko kuma Sheikh Ahmadu Tijjani?
Wannan jami’a za ta koyar da programmes da al’ummar Musulmai suke fama da matsalarsu ne musamman na bangaren likitanci, computer da kuma banking da finance. Maimakon iyalinka, kanwarka ko ’yar uwarka mace ba ta da lafiya namiji ya duba ta, sai ’yar uwarta mace ta duba ta.
Yanzu Dr. Jamilu bai san cewa wasu daga cikin Federal da State Universities da muke da su na gwamnati akwai laccarorin arná masu cewa Annabi Isa (AS) ɗan Allah ne ba? Sannan akwai laccarorin da ’yan darika ne, har a Department na Islam da Arabic Studies, yanzu kenan duk mu daina zuwa waɗannan makarantu saboda kada mu koyi darikanci kenan ya Dr. Jamilu?
Yanzu Dr. Jamilu ya faɗa mana da mu tura ’ya’yanmu Tazkiyah University makarantar mata zalla ta ’yan darika su yi karatun boko, da kuma mu tura su makarantu maza da mata da wasu daga cikin laccarorin ta arná ne domin su yi karatun boko, wannene ya fi?
Idan kace dole ma sai ka yi magana, to sai ka yi wa mata nasiha cewa karatun boko kuka je yi, ba ruwanku da darikarsu, ku yi ilimi boko ku aje musu darikarsu. Ina ga ta ya fi maka alkairi.