Karatuttukan Malaman Musulunci

Karatuttukan Malaman Musulunci ​Welcome! I am a digital creator providing original commentary and educational breakdowns of Islamic lectures. Contact: [email protected]
(5)

I offer unique perspectives on clerics' teachings through deep analysis and daily reflections.

Masarautar Zazzau ta dakatar da Sheikh Khamis Almisiry, limamin Juma’a na masallacin Abu Ubaida Bin Jarrah da ke Tudun W...
30/04/2026

Masarautar Zazzau ta dakatar da Sheikh Khamis Almisiry, limamin Juma’a na masallacin Abu Ubaida Bin Jarrah da ke Tudun Wada a jihar Kaduna, tare da na’ibinsa Malam Aminu Garba.

Limaman da za su jagoranci Sallar Juma’a a Masallatai Biyu Masu Tsarki:Masallacin Harami (Masjid Al-Haram):  Sheikh Dr. ...
30/04/2026

Limaman da za su jagoranci Sallar Juma’a a Masallatai Biyu Masu Tsarki:

Masallacin Harami (Masjid Al-Haram): Sheikh Dr. Ahmad bin Ali al-Hudhaify.

Masallacin Annabi (Masjid Al-Nabawi): Sheikh Osama bin Abdullah Khayyat

01 Mayu 2026 | 13 Zul Qa'ada 1447

Wasu sun ce ina cin mutunci Dr. Jamilu Aliyu Waziri, wasu kuma s**a ce ni munafiki ne, wasu kuma s**a ce ni ne mai haɗa ...
30/04/2026

Wasu sun ce ina cin mutunci Dr. Jamilu Aliyu Waziri, wasu kuma s**a ce ni munafiki ne, wasu kuma s**a ce ni ne mai haɗa rikici tsakanin Ahlussunnah 😂

A jiya fa cikin martanin Dr. Jamilu ga Sheikh Anas ya furta waɗannan kalmomi a ƙasa da awa ɗaya. Shin dan Allah waye mai cin mutuncin mutane kenan tsakanin ni da Dr. Jamilu?

- Jani talau
- Ɗan aiken ƙungiya da ƙungiyanci
- Malamai da kake bautarsu
- Malamai da ka mayar gumaka kake bauta musu x3
- Ba ka jin tsoron Allah
- Jikan ɗan ubaiyu
- Maganar da kake yi alama ce ta munafunci
- Allah ya tsine wa mai ƙarya tsakanin ni da kai x3
- Saboda munafunci
- Jani talau ɗin ƙungiya
- Ɗan ubaiyu bn Salul

Mu fara fadawa Dr. Jamilu ya daina cin mutunci mutane da sunan raddi.

Sheikh Ibrahim Aliyu Kaduna ya yaba wa Prof. Maqari tare da yi masa addu’a kan samar da jami’ar mata zalla a garin Zaria...
30/04/2026

Sheikh Ibrahim Aliyu Kaduna ya yaba wa Prof. Maqari tare da yi masa addu’a kan samar da jami’ar mata zalla a garin Zaria mai suna Tazkiyah University Kaduna. Sannan ya yi kira ga Malaman Izala da su rigangeniya a irin wannan aikin domin share wa Musulmai hawaye.

Dr. Jamilu ya yi raddi ga Sheikh Ibrahim Kaduna akan wannan yabo da addu’a da ya yi wa Prof. Maqari tare da cewa kome ɗan bidia ya yi ba a yabonsa, domin wannan makaranta ma koyarwa da bautar Annabi da shehunai za a yi koyar. 😂

Sannan ya ce saboda darika ta fara mutuwa aka shigo da wannan yaudara ta jami’ar mata zalla, kana Ahlussunnah ka ɗauki yarka ka kai ta sai a koya mata darika ta haifi ’ya’ya duk su zama ’yan darika.

Abin takaici Dr. Jamilu bai iya isar da sakonsa ba sai da ya furta waɗannan kalmomi cikin vedion da ba fi minti biyar ba, ga su kamar haka;
1. Rubabbun malamai
2. Rashin hangen nesa
3. Mai ƙarancin tunani
4. Mai ƙarancin hangen nesa
5. Kwadayi ya mamaye zuciyarsu ba sa gane fari da baki
6. Kwaram da ci da addinin Malaman Ahlussunnah s**a saka a gaba
7. A ci da addini an ci da addini

Dan Allah wannan sunansa raddi ko cin mutunci? Kuma abin takaici shi ne Dr. Jamilu bai san ma wacce kalar jami’a Prof. Maqari ya samar ba wallahi.

A hoto na sama ga “about” din Tazkiyah University nan, sannan ga take off faculties and programmes da wannan jami’a da za ta gudanar. Dan Allah a ina ne aka ce za a koyar da Diwani, Jawahirul Ma’ani, Salatul Fati, tarihin rayuwar Sheikh Inyass ko kuma Sheikh Ahmadu Tijjani?

Wannan jami’a za ta koyar da programmes da al’ummar Musulmai suke fama da matsalarsu ne musamman na bangaren likitanci, computer da kuma banking da finance. Maimakon iyalinka, kanwarka ko ’yar uwarka mace ba ta da lafiya namiji ya duba ta, sai ’yar uwarta mace ta duba ta.

Yanzu Dr. Jamilu bai san cewa wasu daga cikin Federal da State Universities da muke da su na gwamnati akwai laccarorin arná masu cewa Annabi Isa (AS) ɗan Allah ne ba? Sannan akwai laccarorin da ’yan darika ne, har a Department na Islam da Arabic Studies, yanzu kenan duk mu daina zuwa waɗannan makarantu saboda kada mu koyi darikanci kenan ya Dr. Jamilu?

Yanzu Dr. Jamilu ya faɗa mana da mu tura ’ya’yanmu Tazkiyah University makarantar mata zalla ta ’yan darika su yi karatun boko, da kuma mu tura su makarantu maza da mata da wasu daga cikin laccarorin ta arná ne domin su yi karatun boko, wannene ya fi?

Idan kace dole ma sai ka yi magana, to sai ka yi wa mata nasiha cewa karatun boko kuka je yi, ba ruwanku da darikarsu, ku yi ilimi boko ku aje musu darikarsu. Ina ga ta ya fi maka alkairi.

Dr. Jamilu ya zargi Mal. Anas da cakuda zance, amma ya tabbatar da cewa an tara kuɗi. Ya yi rantsuwa da Allah cewa wanna...
29/04/2026

Dr. Jamilu ya zargi Mal. Anas da cakuda zance, amma ya tabbatar da cewa an tara kuɗi. Ya yi rantsuwa da Allah cewa wannan kuɗin an tara su ne domin Mal. Yusuf, ba domin Dr. Idris ba, kuma kuɗin naira 22k ne kacal. Kuɗin kuma an yi amfani da su ne domin hidimar Mal. Yusuf akan kamun da akai masa na farko shekara uku da s**a huce.

😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂😂

Gaskiya Dr. Jamilu baiji dadin wannan abu ba, an saka shi bayani dalla dalla cikin daren nan.

Yanzu ƙarfe 9:45 na dare, kamar yadda Dr. Jamilu ya yi alƙawarin raddi ga Sheikh Anas Idris da misalin ƙarfe 9:30, muna ...
29/04/2026

Yanzu ƙarfe 9:45 na dare, kamar yadda Dr. Jamilu ya yi alƙawarin raddi ga Sheikh Anas Idris da misalin ƙarfe 9:30, muna sanar da Dr. Jamilu dan Allah kafin a fara raddin a yi mana bayani shin da gaske account ɗinka ne, idan naka ne shin an tura kuɗaɗen, idan an tura kuɗaɗen shin naira nawa aka tura maka, sannan ya ka yi da kuɗaɗen da aka tura maka.

Idan an ba mu waɗannan amsoshin, to sai a shiga raddin. Dan Allah kada a zo a yi mana waske-waske ba tare da an ba mu waɗannan amsoshin ba.

Domin gaskiya abun ya daure mana kai ace wai Dr. Jamilu ne ya yi ƙwaram 😂

Bayan Dr. Jamilu ya gama bayanin yadda ya yi da kuɗin da aka tura masa ta account dinsa, to nima ina son ƙarin bayani ka...
29/04/2026

Bayan Dr. Jamilu ya gama bayanin yadda ya yi da kuɗin da aka tura masa ta account dinsa, to nima ina son ƙarin bayani kan hukuncin saka hoto a WhatsApp DP 😄

Abu biyu, sai zuba ido nake na gano account din Dr. Jamilu nima na saka 5k ɗin ta domin na sha addu’a amma ban gani ba. Wanda ya gani ya ajemin a kwamen Sakshin.

Abu na uku, dan Allah Mal. Anas a rufe wannan ƙofar haka, tunda an shafa kansa ya isa haka dan Allah.

28/04/2026

“Kuna ji ko, idan za'a yi aure ayi mata screening sosai kada a bawa ɗan Izala.”
Baba Arzai 😂

28/04/2026

Barr. Ishaq Adam Ishaq

28/04/2026

Ku saurara kuji ya ku yan siyasa.

Shiekh Adam Abdullah Dorayi

Hoto: Ziyarar Mal. Bashir Ahmad Sani Sokoto wajen babban malamin addinin Musulunci, Shaikh Bello Yabo a yau Litinin 27 g...
27/04/2026

Hoto: Ziyarar Mal. Bashir Ahmad Sani Sokoto wajen babban malamin addinin Musulunci, Shaikh Bello Yabo a yau Litinin 27 ga watan Afrilu, shekara ta 2026.

27/04/2026

Sakon Shiekh Ibrahim Alhassan Saeed Adam ga Gidan Jaridar Mikiya da s**a yada fake news a kansa, tare da matsayarsa akan APC/ADC.

Address

Kano
Kano
700101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karatuttukan Malaman Musulunci posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Karatuttukan Malaman Musulunci:

Share