28/04/2024
IYAYEN ANNABI MUHAMMADU
(SAW) 'YAN ALJANNA NE
Wasu mutane sun dauki kayan talla domin sayarwa a madadin IBLIS (L.A.) . Kayan da Shaydan din kuwa ya dora masu a kansu domin su sayar masa shi ne CIN MUTUNCIN MANZON ALLAH (SAW) , wato halittar nan mai albarka , wadda Shaydan ya fi kin ta a cikin halittun Allah (SWT) .
Kowane mai talla da abin da yake fada a lokacin talla domin ya jawo hankalin mutane zuwa ga kayan
da yake so a saya . Su masu wannan talla, a madadin Shaydan , abinda suke cewa shi ne " IYAYEN ANNABI
'YAN WUTA NE . " Allah (SWT) Ya tsare mu . Innaa lil-Laahi , wa innaa ilayhi raaji'uun !
SAKAMAKON DA WANNAN TALLA ZAI HAIFAR Duk wanda ya yarda da cewa
iyayen Manzon Allah (SAW) 'yanwuta ne , wato kafirai ne , to zai samu kansa cikin :
i . karyata Allah (SWT) ;
ii. karyata Manzon Allah (SAW) ;
iii. cutar da Allah (SWT), da kuma ManzonSa (SAW) .
SAKAMAKON DA MASU TALLA DA SAYEN WANNAN KAYA ZASU SAMU
Mafi kankantar sakamakon da masu cewa iyayen Manzon Allah (SAW) , Abdul-Laahi da Aaminatu (A.S.), 'yan wuta ne , da wadanda s**a yarda da haka , zasu samu shi ne
zama a katafaren gidan Shaydan, wato WUTA . Allah (SWT) Ya tsare mu .
Zasu samu wannan sakamako ne sanadiyyar karyata Allah (SWT) , karyata Manzon Allah (SAW) , da
kuma cutar da Allah (SWT) da
ManzonSa (SAW) . Insha'Allah , zamu ji yadda fadin haka yake karyata Allah (SWT) da ManzonSa (SAW) , da kuma cutar da su .
DALILAN DAKE NUNA CEWA
IYAYEN MANZON ALLAH (SAW) BA 'YAN WUTA BA NE
Akwai dalilai masu nuna cewa
iyayen Manzon Allah (SAW) ba 'yan wuta ba ne . Dalilan kuwa su ne :
i. dalilai daga Al-Qur'ani ,
ii. dalilai daga Hadisi , da kuma
iii. dalilai na hankali .
Abin mamaki ne a ce musulmi- mai-hankali ya yarda , kuma har ya rika fadin cewa iyayen Shugaban manzanni (A.S.) , kuma
halittar da Allah(SWT) Ya fi so a cikin dukkan halittarSa , "'yan wuta ne ." A'uudhu bil-Laah ! A dalilin wannan gawurtaccen rashin hankali da masu fadi , da kuma
yarda da wannan mummunar
magana , ke nunawa zan fara
amfani da dalilai na hankali domin kifar da wannan kaya na talla da Shaydan (L.A.) ya dora wa masu tallan kayansa domin su sayar masa .
DALILAI NA HANKALI MASU NUNA CEWA IYAYEN MANZON ALLAH (SAW) BA 'YAN WUTA BA NE
Akwai dalilai , masu yawa ,na
hankali masu nuna cewa iyayen Manzon Allah (SAW) , Abdul-Laahi (AS) , da Aminatu (AS) , ba 'yan wuta ba ne . Daga ciki akwai :
i. sunayensu (AS) : sunan mahaifin Manzon Allah (SAW) Abdul-Laahi , wato BAWAN ALLAH . Sunan mahaifiyarsa Aaminatu , wato WADDA TA YI IMANI. Idan mutum yana da lafiyayyen hankali , zai gane cewa lallai Allah (SWT) Ya kimsawa iyayensu ne su sa masu wannan suna saboda ya san zasu kasance
mutane ne muminai wadanda zasu haifi shugaban manzanni (SAW) .
A wancan lokaci , babu mutane masu suna Abdul-Laahi , da Aaminatu , a cikin mushirikai .
ii. iyayen dukkan Annabawa (AS) muminai ne : dukkan Annabawa , har da Annabi Ibraahiim (AS) , iyayensu ba kafirai ba ne . Saboda haka , mai lafiyayyen hankali zai
fahimci cewa iyayen Manzon da ya fi dukkan Manzanni komai , a wurin Allah (SWT) , baza su zama
a ce su kadai ne kafirai ba, 'yan wuta . A'uudhu bil- Laah !
Misali : Babu yadda za a yi a ce kwamishinoni nada motar ofis , amma gwamna baida ita .
iii. duk iyayen Annabawa(AS) 'yan Aljanna ne : Mai hankali zai fahimci cewa babu yadda za a yi a ce kowane manzo zai zauna tare da iyayensa a Aljanna , amma Shugabansu nasa iyayen na wuta .
iv. duk wanda ya shiga Aljanna. ya shiga ne saboda sakamakon bin sakon da Manzon Allah(SAW) ya kawo :
mai hankali zai fahimci cewa babu yadda za a yi a ce duk alherin nan da Manzon Allah (SAW) ya zo da shi , amma kuma a ce iyayensa (AS) ba zasu amfana ba, saidai su zauna a wuta tare da Shaydan, Abuu Jahlin , Abuu Lahbin , Fir'aun, da sauran kafirai.
Misali : Attajiri , kuma mutumin kirki , mai ba talakawa abinci , an ya zai hana iyayensa abinci , har su mutu saboda yunwa ?
v. Makkah da Madinah sun fi
kowane gari ne saboda an haifi Manzon Allah (SAW) ne a Makkah, kuma ya tafi gidan rahama a Madinah : mai hankali zai fahimci
cewa yadda garin da aka haifi
Manzon Allah (AS) ya fi kowane gari , haka tsatso , da kuma cikin da Manzon(SAW) ya zauna ya fi kowane tsatso da ciki. Saboda haka , mai tsatson , da kuma mahaifar da Manzon Allah (SAW) ya zauna , wato Abdul-Laahi (AS) , da Aaminatu (AS) , sun fi iyayen kowa, dalilin haka su ba 'yan wuta ba ne .
vi. mushirikai kazanta ne : Saboda haka , babu yadda za a yi a ce Allah (SWT) Ya sanya Manzon Allah (SAW) , halittar da Ya fi so , a cikin kazanta , wato tsatso da mahaifa
ta mutane kafirai . Wannan yana nuna wa mai hankali cewa mai tsatso da mahaifar da Annabi (SAW) ya zauna , wato iyayensa (AS) , ba
kafirai ba ne , domin su ba najasa ba ne .
Zan tsaya a nan yau . Insha' Allah gobe ko jibi , zan kawo wasu daga cikin dalilai na Hadisi masu nuna cewa iyayen Manzon Allah (AS) ba 'yan wuta ba ne kamar
yadda Shaydan ya bayar da talla ga wasu , kuma suke yi.
Allah (SWT) Ya kara wa Manzon Allah (SAW) alayensa(AS) , da sahabbansa (RA) , tsira da aminci .