30/01/2026
MADOGARAR HUKUNCE-HUKUNCEN SHARI'A A WURIN SHI’A.
Ba kawai Musulmai ba har wasu daga cikin kafurai sun yarda cewa shara’ar Musulunci wacca Annabi Muhammad ﷺ Ya zo da ita madogararta su ne Kur’ani da Hadisan Annabi ﷺ.
Kamar yadda Malaman Musulunci s**a tabbatar Madogarar shari’a wanda Malamai s**a haɗu a kai su ne: Qur’ani, Hadisi, Ijma’i sai Qiyasi wannan ba ma iya Malaman Ahlus Sunnah ba har da wasu daga cikin Malaman sauran Ƙungiyoyi karkatattu suna tabbatar da wannan.
To amma abin mamaki shi ne, ƙungiyar Shi’a basu da alaƙa ta kusa ko ta nesa da waɗannan madogarar shara’a wacca Musulmai ke kai.
Sannan duk wata hanya da zata kaisu zuwa kan nassoshin shara’ar Musulunci sun datse ta, misali, Shi’a suna riyawa cewa dukkan Sahabban Annabi ﷺ sun yi ridda bayan mutuwarSa, kamar yadda babban malaminsu Muhammad bin yaƙub Alkulainiy cikin littafinsa (Furu’ul kahfi), ya ce: “an ruwaito daga Ja’afar amincin Allah su tabbata a gare Shi Ya ce: dukkanin mutane ma’abota ridda ne, bayan Annabi ﷺ , sai guda uku, sai na ce su wanene guda ukun? Sai ya ce, su ne: Miqdadi binil Aswad, da Abu zarril Gifari, da Salmanul Farisi”, Wa iyazu billah! ‘yan uwa wannan fa ƙaramin misali ne daga cikin cin mutunci da sharri da Shi’a suke yiwa sahabban Annabi ﷺ, wanda in sha Allahu magana akan hakan zai zo nan gaba.
To kunga kenan a nan ba yadda za a yi Shi’a su yarda da Nassoshin addinin Musulunci, tunda Sahabban Annabi ﷺ su ne su ka naƙalto dukkanin waɗannan Nassoshin, kuma su a wurinsu Sahabban Annabi kafurai ne, don haka babu ta yadda za a yi su karɓi addini a hannun kafurai.
Babu shakka Shi’a su na da nasu madogarar ta daban, inda su ke tsamo hukunce-hukuncensu wadda ya sha bam-bam da wadda musulmai suke kai. Idan me tambaya ya ce, to waɗanne ne madogarar? Amsa shi ne: An ruwaito daga litattafan da ‘yan Shi’a su ke dogaro dasu wurin tsamo hukunce-hukunce cewa, akwai Qur’ani da su ka yarda da shi, koma-bayan wanda ya ke hanun musulmai.
"Alkulainiy" ya ruwaito cikin Usuulul Kahfiy daga Ja’afarus Saadiq Ya ce: “lallai a wurinmu akwai “Mushafu Faɗima” (Qur’anin Fatima) amincin Allah Ya tabbata a gareTa, ya ce: sai na ce menene Qur’anin Faɗima, sai Ya ce: Qur’ani ne wanda Ya ninka Qur’aninku ninki uku, ina rantsuwa da Allah babu harafi ɗaya a cikin shi dake cikin Qur'aninku”.
Sannan su na da litattafai da su ka dogara da su a fannin Hadisai da Fiqhu, wadda su waɗannan litattafai sun ƙunshi Maganganun Limamansu da maganganun Manyan malamansu. Shi yasa idan ka bibiyi aƙidun Shi’a, da yadda suke gudanar da addininsu zaka samu akwai tufka da warwara a ciki, kuma haka zalika suna cin karo da Addinin Musulunci.
Daga cikin litattafan da Shi’a suke dogaro da su wurin Aƙidu, da hukunce-hukunce d.s, akwai: Qur’anin da suke yi wa laƙabi da Qur’anin Fatima kamar yadda magana akan shi ya gabata, sai littafin, Usulul Kahfi na Kulaini, wanda matsayin shi a wurinsu kamar matsayin Sahihul Bukhari ne a wurin Ahlus Sunnah, sai littafin: Man La Yahduruhul Faqih na Ibnu Babawaihil Qummi, sai Tahzibul Ahkam Fi sharhil Muqni’i na Muhammad Bin Hasan Aɗɗusiy, sai Al’istibsar fi makhtalafa Minal Khabar, shima wallafar Aɗɗusiy, da ma sauran litattafansu wanda in Allah Ya yarda zamu jerosu nan gaba, waɗanda mafi yawan abin da ke ciki ƙarairayi ne da shirme.
Ko da yake wasu daga cikin Shi’a suna nesanta kansu da waɗannan litattafan domin irin abubuwa da ke ciki wanda ke cin karo da Shara’ar Musulunci da kuma lafiyayyar hankali. Sannan wasu daga cikinsu suna ƙin waɗannan litattafan ne domin sun jahilci haƙiƙanin da’awar Shi’a, ko kuma sun tsinci kansu ne a cikinta ba tare da sun san aƙidunsu ba. Wasu kuma daga cikinsu suna inkari ne a zahiri amma sun ɓoye haƙiƙanin gaskiya a cikin ransu, wato suna taƙiyya.
Sannan game da Qur’ani wasu daga cikin Malamansu suna riya cewa wannan Qur’anin da ke hanun Musulmai an yi ƙarin wasu ayoyi kuma an rage wasu kamar yadda su ke riya cewa su na da Qur’ani wanda ya sha bam-bam da na Musulmai kamar yadda zance ya gabata.
Sai dai a nanma Malaman Shi’a sun sassaɓa yayin da wasu suna ganin lallai an yi ragi da ƙari a cikin Qur’ani wasu kuma suna ganin saɓanin haka wasu kuma suna ƙaryata malaman farko.
Aliyu Assalafy