TFS Islamic Channel

TFS Islamic Channel wannan Channel mai suna TFS wato Tadbiƙu Ilmus Salaf an ƙirƙire shi ne don wayar da kan al'umma game

17/02/2026

A cewar hukumomin Saudiyya, za a tashi da azumin Ramadana na shekarar Musulunci ta 1447 a kasar a gobe Laraba 18 ga watan Fabrairu, 2026.

17/02/2026
01/02/2026

Daga Bunyamin Aliyu Assalafy

LITATTAFAN SHI'A DA MAWALLAFANSU (02)

[ ] Litattafan Hadisi:

1. Usuulul kaafi: wallafar Sheikh Abu Ja’afar Muhammad bin Ya’qub Al-kulainiy wanda ya mutu hijira na 329 H. Shi wannan littafi ya ƙunshi kimanin Hadisai dubu goma sha shida da ɗari da casa’in (16,190), an kasa littafin gida uku kamar haka: Usul, Furu’, Raudha.
Kaso na farko wato “usuulul kaafi” ya ƙunshi Hadisai da ke Magana akan aƙida da imama, sannan shi kuma “furu’ul kaafi” ya ƙunshi Hadisai da ke Magana akan Fiqhu da hukunce-hukunce, shi kuma “raudhatul kaafi” ya ƙunshi Hadisai mabambanta. Sannan shi wannan littafi madogara ne babba a wurin Rafidawa, sannan kusan duk malaman rafidawa da s**a zo bayan shi mawallafin wannan littafin sun yaba masa sosai da irin ƙoƙarin da yayi wurin haɗa wannan littafi na “usulul kaafi”, har suna riya cewa babu wani littafin Hadisi da ya kai shi inganci, wato dai kamar yadda al’ummar Musulmi s**a yarda cewa babu wani Littafin da aka tattara Hadisan Annabi ingantattu irin Littafin "Sahihul Bukhari", haka suma Rafidawa s**a yarda da littafin Usuulul Kaafi.

2. Man la yahdhuruhul Faqih: wallafar Muhammad bin Aliyu bin Babawaihi Al-qummiy, wanda aka fi sani da Shaikhus Saduq, ya mutu a shekara ta 381 H. shi wannan littafi ya ƙunshi Hadisai 5973 kamar yadda aka kawo a cikin shimfiɗar Littafin “wasa’ilush shi’a”.

3. Attahzibul Ahkam: wallafar Sheikhuɗ ɗa’ifa Abu Ja’afar Muhammad bin Hassan bin Aliyu bin Hassan Aɗɗusiy, an haife shi a shekara ta 385 H, ya mutu a 460 H. Kamar yadda ya zo a shimfiɗar littafin "Wasa'ilush Shi'a" : littafin Tahzibul ahkam na Aɗɗusiy, ya zarce sauran litattafan hadisai wurin kawo hadisan furu’a (fiqhu), waninsa ba zai isar ba in ba shi ba a wannan fannin.
Sannan shi wannan littafi sharhi ne na littafin “Almuqni’a” na shehin Malami "Almufid", wanda malami ne ga Muhammad bin Hassan Aɗɗusiy. Littafin “Tahzib” ya ƙunshi babuka 390, sannan hadisan ciki sun kai guda 13,590.

4. Al’istibsar: shima wallafar Muhammad bin Hassan bin Aliyu bin Hassan Aɗɗusiy. Shi kuma ya ƙunshi babuka guda 915 ko 925, sannan Hadisan cikin sun tasamma 5511.

5. Alwaafiy: wallafar Murtadha bin Mahmud, wanda aka fi sani da Maula Muhsin Al-kaashaniy kuma ake masa laƙabi da Faidhul kaashaniy.
An haife shi 1007 H, ya kuma rasu shekara ta 1091 H.

6. Biharul Anwaar: wallafar shehin malami Baaƙir bin Sheikh Muhammad Taqiyyu Al-majlisiy. An haife shi 1037 H ya mutu 1110 H.
Littafin Biharul Anwar littafi ne da aka tattara Hadisai masu tarin yawa. Ya rattaba wa littafin babuka sannan ko wani babi yana kawo Ayar Qur’ani da take da munasaba da babin, sannan ko wani hadisi ya na yi mishi taqaitaccen sharhi da fassarar kalmomi.

7. Wasa’ilush shi’a: wallafar Sheikh Muhammad bin Hussain bin Aliyu Hurrul Aamiliy, an haife shi 1033 H, ya mutu 1104 H. Shi wannan Littafi ya ƙunshi wasu daga cikin hadisan da s**a zo daga (kutubul arba’a) wato Litattafai huɗu, waɗanda sune madogarar hukun-hukunce da ya shafi Hadisi, da ma wasu daga cikin litattafan hadisi na Rafidhawa.

31/01/2026

Daga Bunyamin Aliyu Assalafy

LITATTAFAN SHI’A DA MAWALLAFANSU (01)

Kamar yadda muka kawo a baya cewa Shi’a basu yarda da mafi yawan nassoshin Addinin Musulunci ba, kuma basu yarda da cewa Qur’ani da ke hannun Musulmai shi ne wanda Allah Ya sauƙar wa Annabi Muhammad ﷺ ba. Haka nan Litattafan da muke amfani dasu, suma basu yarda da su ba, su na da nasu litattafan na daban wanda ya sha bam-bam da wanda ke hannun Musulmai kamar yadda muka fara nuni akansu a baya, zamu kawosu ɗaya bayan ɗaya.

Litattafan Rafidawa suna nan fanni-fanni kamar yadda bincike ya tabbatar, wato akwai Litattafan tafsiri, akwai na Hadisi akwai na fiqhu da sauransu, sai dai mu zamu taƙaita ne wurin kawo litattafansu da s**a shahara.

[ ] Litattafan Tafsiri:

1. Tafsirul Qummiy: wallafar Sheikh Aliyu bin Ibrahim AlQummiy, ya mutu a shekarar 307H, kuma ɗaya daga cikin manyan malaman shi’a a ƙarni na uku sannan ɗaya daga cikin malamai a babban makarantar “Qum” , malami ne na tafsiri da Hadisi a wurin shi'a.

2. Tafseerul mizaan: wallafar Muhammad Husain aɗɗabaɗaba’iy, an haife shi a shekara ta 1321 H a garin Tibriz da ke ƙasar Iran, ya kuma mutu a shekara ta 1402 H, yana daga ciki manyan malaman addini da falsafanci a wurin Shi’a.

3. Tafsirul Ayyashiy: wallafar Muhammad bin Mas’ud Al-ayyashiy Assamaraqandiy, asalinsa ɗan samaraqand ne, ya mutu a shekara ta 320 H, yana da matsayi na ilimi mai girma a wurin Rafidhawa.

4. Tafsirus Saafiy: wallafar Al-faidhul Kaashaniy, cikakken sunansa Mulla Muhisin Muhammad bin Murtadha Alkaashaniy, an haife shi a shekara ta 1007 H, ya mutu 1091 H. malami ne na Fiqhu,Tafsiri, Falsafa da Hadisi sannan fitacce a wurin shi'a.

5. Majma’ul Bayan fi Tafsiril Qur’an: wallafar Aɗɗabrisiy wanda ya rasu hijira na 548 H, cikakken sunansa Sheikh Aminul Islam Al-fadhlu bin Hassan Aɗɗabrisiy.

30/01/2026

MADOGARAR HUKUNCE-HUKUNCEN SHARI'A A WURIN SHI’A.

Ba kawai Musulmai ba har wasu daga cikin kafurai sun yarda cewa shara’ar Musulunci wacca Annabi Muhammad ﷺ Ya zo da ita madogararta su ne Kur’ani da Hadisan Annabi ﷺ.
Kamar yadda Malaman Musulunci s**a tabbatar Madogarar shari’a wanda Malamai s**a haɗu a kai su ne: Qur’ani, Hadisi, Ijma’i sai Qiyasi wannan ba ma iya Malaman Ahlus Sunnah ba har da wasu daga cikin Malaman sauran Ƙungiyoyi karkatattu suna tabbatar da wannan.

To amma abin mamaki shi ne, ƙungiyar Shi’a basu da alaƙa ta kusa ko ta nesa da waɗannan madogarar shara’a wacca Musulmai ke kai.
Sannan duk wata hanya da zata kaisu zuwa kan nassoshin shara’ar Musulunci sun datse ta, misali, Shi’a suna riyawa cewa dukkan Sahabban Annabi ﷺ sun yi ridda bayan mutuwarSa, kamar yadda babban malaminsu Muhammad bin yaƙub Alkulainiy cikin littafinsa (Furu’ul kahfi), ya ce: “an ruwaito daga Ja’afar amincin Allah su tabbata a gare Shi Ya ce: dukkanin mutane ma’abota ridda ne, bayan Annabi ﷺ , sai guda uku, sai na ce su wanene guda ukun? Sai ya ce, su ne: Miqdadi binil Aswad, da Abu zarril Gifari, da Salmanul Farisi”, Wa iyazu billah! ‘yan uwa wannan fa ƙaramin misali ne daga cikin cin mutunci da sharri da Shi’a suke yiwa sahabban Annabi ﷺ, wanda in sha Allahu magana akan hakan zai zo nan gaba.

To kunga kenan a nan ba yadda za a yi Shi’a su yarda da Nassoshin addinin Musulunci, tunda Sahabban Annabi ﷺ su ne su ka naƙalto dukkanin waɗannan Nassoshin, kuma su a wurinsu Sahabban Annabi kafurai ne, don haka babu ta yadda za a yi su karɓi addini a hannun kafurai.

Babu shakka Shi’a su na da nasu madogarar ta daban, inda su ke tsamo hukunce-hukuncensu wadda ya sha bam-bam da wadda musulmai suke kai. Idan me tambaya ya ce, to waɗanne ne madogarar? Amsa shi ne: An ruwaito daga litattafan da ‘yan Shi’a su ke dogaro dasu wurin tsamo hukunce-hukunce cewa, akwai Qur’ani da su ka yarda da shi, koma-bayan wanda ya ke hanun musulmai.

"Alkulainiy" ya ruwaito cikin Usuulul Kahfiy daga Ja’afarus Saadiq Ya ce: “lallai a wurinmu akwai “Mushafu Faɗima” (Qur’anin Fatima) amincin Allah Ya tabbata a gareTa, ya ce: sai na ce menene Qur’anin Faɗima, sai Ya ce: Qur’ani ne wanda Ya ninka Qur’aninku ninki uku, ina rantsuwa da Allah babu harafi ɗaya a cikin shi dake cikin Qur'aninku”.

Sannan su na da litattafai da su ka dogara da su a fannin Hadisai da Fiqhu, wadda su waɗannan litattafai sun ƙunshi Maganganun Limamansu da maganganun Manyan malamansu. Shi yasa idan ka bibiyi aƙidun Shi’a, da yadda suke gudanar da addininsu zaka samu akwai tufka da warwara a ciki, kuma haka zalika suna cin karo da Addinin Musulunci.

Daga cikin litattafan da Shi’a suke dogaro da su wurin Aƙidu, da hukunce-hukunce d.s, akwai: Qur’anin da suke yi wa laƙabi da Qur’anin Fatima kamar yadda magana akan shi ya gabata, sai littafin, Usulul Kahfi na Kulaini, wanda matsayin shi a wurinsu kamar matsayin Sahihul Bukhari ne a wurin Ahlus Sunnah, sai littafin: Man La Yahduruhul Faqih na Ibnu Babawaihil Qummi, sai Tahzibul Ahkam Fi sharhil Muqni’i na Muhammad Bin Hasan Aɗɗusiy, sai Al’istibsar fi makhtalafa Minal Khabar, shima wallafar Aɗɗusiy, da ma sauran litattafansu wanda in Allah Ya yarda zamu jerosu nan gaba, waɗanda mafi yawan abin da ke ciki ƙarairayi ne da shirme.

Ko da yake wasu daga cikin Shi’a suna nesanta kansu da waɗannan litattafan domin irin abubuwa da ke ciki wanda ke cin karo da Shara’ar Musulunci da kuma lafiyayyar hankali. Sannan wasu daga cikinsu suna ƙin waɗannan litattafan ne domin sun jahilci haƙiƙanin da’awar Shi’a, ko kuma sun tsinci kansu ne a cikinta ba tare da sun san aƙidunsu ba. Wasu kuma daga cikinsu suna inkari ne a zahiri amma sun ɓoye haƙiƙanin gaskiya a cikin ransu, wato suna taƙiyya.

Sannan game da Qur’ani wasu daga cikin Malamansu suna riya cewa wannan Qur’anin da ke hanun Musulmai an yi ƙarin wasu ayoyi kuma an rage wasu kamar yadda su ke riya cewa su na da Qur’ani wanda ya sha bam-bam da na Musulmai kamar yadda zance ya gabata.

Sai dai a nanma Malaman Shi’a sun sassaɓa yayin da wasu suna ganin lallai an yi ragi da ƙari a cikin Qur’ani wasu kuma suna ganin saɓanin haka wasu kuma suna ƙaryata malaman farko.

Aliyu Assalafy

29/01/2026

QUNGIYAR SHI’A, DA BAYYANARTA

Shi’a ɗaya ce daga cikin ƙungiyoyi da suke danganta kansu da Addinin Musulunci, kuma suna iƙirarin son iyalan gidan Annabi ﷺ. Kuma ita ce ƙungiya ta biyu da ta bayyana daga cikin ƙungiyoyin ɓata, sannan suna da wasu aƙidu nasu wadda ya sha bam-bam da sauran ƙungiyoyi, kuma suna riya cewa Aliyu Allah Ya yarda da Shi, Shi ya cancanci halifanci bayan mutuwar Annabi tsira da aminci su tabbata a gare Shi ba Abubakar ba.

An naƙalto daga babban Malami "Ibnu Hazam", a cikin littafinsa (Alfaslu fil Ahwa’i wal milal wan Nihal) yana cewa: “Ƙungiyar Shi’a ta bayyana ne ta ƙarshe-ƙarshen zamanin halifancin Usman ɗan Affan Allah ya yarda da shi”.

"Sheikh Abdullahi bin Muhammad Assalafiy" a cikin littafinsa mai suna (Min Aqa’idish Shi’a) ya ce: “Qungiyar Shi’a ta faro ne yayin da wani mutum Bayahude ya bayyana mai suna Abdullahi bin Saba’a ya yi iƙirarin musulunci, alhali kafuri ne tatacce, shi wannan mutumin yana iƙirarin son Ahlul-baiti, ya kuma wuce gona da iri cikin sha’anin Aliyu Allah Ya yarda da shi, ya kuma yi iƙirarin cewa Aliyu shi ne, wasiyyin Annabi tsira da aminci su tabbata a gare Shi ba Abubakar ba, sannan daga bisani ya ce, ai Aliyu Allah ne”.

Babban Malamin Shi’a wanda ake wa laƙabi da "Ibnu Babawaihil Qummiy" ya ce, a cikin littafinsa mai suna (Almaqalatu wal firaq): “Ana tabbatar da samuwarsa (yana nufin Abdullahi bin Saba’a), kuma ana la’akari da cewa shi ne mutum na farko da ya fara wajabta Halifanci ga Aliyu Allah Ya yarda da shi bayan mutuwar Annabi tsira da aminci su tabbata a gare Shi, da kuma dawowarsa duniya bayan ya mutu. Sannan kuma shi Abdullahi Bin saba’a shi ne ya fara bayyana s**a kan Abubakar, da Umar da Usman da sauran Sahabbai.

31/12/2025

Address

Jalingo
660213

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TFS Islamic Channel posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share