14/10/2025
A karba da hakuri!
Kadan daga cikin banbancin dake cikin harkar Mal. Abduljabbar da ta Mal. Lawal sune:
Mal. Lawal ya bude littafansa, kuma ya karantasu tatas, hasali ma ya kara wa wasu daga cikin yan shura ilimi, domin tabbas wasu basu ci karo da abinda ya karanto ba kafin yau(hakan baya nufin basu da ilimi). Shi kuma Mal. Abduljabbar ko daya bai karanta ba, yace minti 10 ta masa kadan.
Mal. Lawal duk da cewa baâa kureshi ta fuskar hujja ba, amma ya gamsu cewa idan akwai wani salo da yayi wanda ake ganin bai dace ba, to yana mai bada hakuri kuma yana neman gafarar Ubangiji. Kuma nasan tabbas ba zai janye wannan maganar ba.
Mal. Abduljabbar bayan an kureshi ta fuskar dalili, ya kasa bude koda littafi daya a cikin guda 500, yace mintin 10 ta masa kadan. Ya fada da bakinsa cewa yayi laifi, yace don Allah a hakuntashi, ya fito yayi video ya bada hakuri ya nemi yafiyar alâumma. Sai aka samu wasu a cikin irin JARUMAI 500 din da aka tanadar wajen doke Mal. Lawal, s**a zuga Mal. Abduljabbar, sai ya fito yace, zaman tsiyen da aka masa, wasan kwaikwayo ne, an hanashi magana, baisan alkalin ba, an yanke video din zaman da akayi.
Kaga ko da a ce mun yarda duka su biyun sun aikata laifi, Mal. Lawal yayi taubatan nasuha. Mal. Abduljabbar kuma yace yafison doka tayi aikinta. Yace a âdaureshi life of prisonâ (sic)!