30/07/2021
Gwamnatin Jihar Kaduna za ta Daukaka Karar Zakzaky zuwa babban kotun kasa
Gwamnatin jihar Kaduna ta ɗaukaka ƙara akan sakin Sheikh Ibraheem Zakzaky da babban kotun ƙasa dake jihar ta yi a ranar larabar da gabata 28 July 2021.
Mai shari'a Gideon Isa Kurada shi ne alkalin da ya jagoranci wannan shari'a tun da daga farko har ƙarshe, kuma ita gwamnatin jihar Kaduna, ita ce ta shigar da ƙarar Sheikh Zakzaky da mai ɗakinsa a gaban kotu.
An ɗauki kusan shekaru uku ana gabatar da wannan shari'a ɗin, duk da cewa an shaidi al'umma da daman gaske sun shaidi wannan alkalin akan tsattsauran ra'ayi na aiki da tsarin doka ba tareda ƙar6ar cin hanci ba, kuma wanda kuɗi ko ƙarfin iko basu juya shi.
Yanzu dai Nasir Elrufa'i ya ce bai yarda hukuncin ba, kuma zai ɗaukaka ƙara.
Ko me za ku ce kan hakan ?