Slave of ALLAH

Slave of ALLAH Iam proud to be a muslim slave of ALLAH and prophet muhammad lover

28/09/2016

Bakowa bane mutumin banza

Kuma bakowa bane mutumin kirki

Mutun hudu (4) ne kawai nake neman yardarsu

(1) Allahn da yahalicce ni

(2) manzon Allah

(3),,Iyayena

(4) Malamaina

Mutun hudu (4) Suke kaika gahalaka

(1) Zuciya

(2) Shaidan

(3) Mace.

(4) Mummunan aboki

Kada kayarda da abu hudu (4)

(1) Munafiqi

(2) Maci amana

(3) Mahaainci

(4) Makaryaci

Abu hudu (4) yana kawo nasara

(1) Jajircewa

(2) Tausayawa

(3) Tawakkali

(4) Juriya

Abu hudu (4) nakai mutun Wuta

(1) Girman kai

(2) Zalunci

(3) Jahilci

(4). Sa6on Allah

Abu hudu (4) Nakai mutun aljanna

(1) Bin dokokin Allah

(2) Touhidi

(3) Anbatan Allah

(4) Sadaka


Kataimaka da Abu hudu (4)

(1) Alkhairi

(2).Shukashi

(3) Rayashi

(4) Aikatashi

Idan kana son kaxamo mai shuka alkhairi

To duk inda ka ganshi kayi kokarin aikatashi

Allah kabamu daman aikata aikin alkhairi arayuwan mu

10/09/2016

*FITILA GA MASU NUFIN YIN LAYYA:*

FITOWA TA 1

Assalamu alaikum warahmatullahi wa barakatuhu,

Wannan sako ne wanda zai rinka zuwa a takaice na maganganun Malamai dangane da layya wanda na ga dacewar in isar da shi zuwa ga 'yan uwana Musulmi masu nufin yin layya.

*1. Haramcin yanke farce da gashi ga wanda ya yi nufin yin layya:*

An karbo hadisi daga Ummu Salamah, Allah Ta'ala Ya kara yarda a gare ta, ta ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce: *_Duk wanda yake da abun da zai yanka na layya, to matukar jinjirin watan Dhul-Hijja ya k**a, to kada ya yanke komai daga gashinsa ko farcensa, har sai bayan ya yi layya_*. Muslim ne ya riwaito.

*2. Hukuncin wanda ya yanke gashinsa ko farcensa bisa mantuwa:*

Sheikh Muhammad Bn Saleh Al-Uthaimeen, Allah Ta'ala Ya yi masa rahama, ya ce: *_Duk wanda ya yanke gashin kansa ko farcensa bisa mantuwa ko rashin sani, ko gashin shi ya fita ba tare da nufi ba, to babu laifi a gare shi_*.

A duba littafin hukunce-hukuncen layya da zakka na Sheikh Muhammad Bn Saleh Al-Uthaimeen, Rahimahullahu.

*3. Shin hukuncin rashin aski da yanke farce ya kunshi har da wanda za a yi masa layya?*

Sheikh Muhammad Saleh Al-Uthaimeen, Allah Ta'ala Ya yi masa rahama, ya ce: *_Hukuncin rashin aske gashi da yanke farce ya kebanta ne kadai ga wanda ya yi nufin yin layya, amma wanda yi masa za a yi, to babu laifi akansa na yanke farce da aske gashi, dalili kuwa shi ne a cikin hadisin cewa aka yi: "Kuma dayan ku ya yi nufin zai yi layya"_*, don haka sai a takaitu akan abun da nassi ya zo akansa.

Za a iya sauraren wannan a fataawa nurun alad Darb kaset na 93.

*4. Mene ne hukuncin wanda ya yanke gashinsa ko farcensa da gangan?*

Mu haɗu a fitowa ta 2 in sha Allahu Ta'ala.

✍🏼 Dan uwanku a Musulunci:
*_Malam Umar Shehu Zaria_

16/11/2015

Assalamu alaikm warahmatullahi wabara katuhu ayyuhal muslimuun

27/09/2015

Assalamu alaikum my friends how was the holy day i hope you perform your eid-kabir prayer good and normal

05/08/2015

"FALALAR GUSARDA KAZANTA DAGA
KAN HANYA"
(DAGA TASKAR BABAN MARYAM)
DASUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI
JINKAI
FADAKARWARMU TA YAU LARABA
20/SHAWWAL 1436
Zatayi Magana Akan:-
(GUSARDA KAZANTA DAGA KAN
HANYA)
Gusarda Kazanta Daga Kan Hanya
shine Gusarda Dukkan Abinda Zai
Iya Cutarda Jama'a Daga Kan Hanya
Ko kuma Wani Wurinda Jama'a Ke
Ta'ammali Dashi
Wannan Dabi'a Tana Cikin Rassan
Imani Kuma Tana Cikin Ayukkanda
Ake Rubutama Mutum Ladar
Sadaka Idan Ya Aikatasu
Wannan Aikin
(Gusarda kazanta Daga Kan Hanya)
Ana Iya Samun Babban Arziki Wato Shiga Aljanna
Ta Hanyarsa Kamar yadda Yazo Acikin Wani Hadisi
Kamar Haka:-
Manzon Allah Tsira Da Aminci Su
Tabbata Agareshi Yace:-
Naga Wani Mutum Ya Kai Da Kawo
Acikin Aljanna Akan Wata Ittanya
Da Ya Sare A Tsakkiyar Hanya
Wadda Ta Kasance Tana Cutarda
Jama'a
(Muslimu Ya Ruwaitoshi)
idan Muka Dubi Wannan Hadisi
Duba Na Basira Zai Nunamana
Muhimmanci Da Falalar Wannan
Aikin
TAREDA FATAN ZAMU KIYAYE
ALLAH YABAMU IKON KIYAYEWA
BISAGA IKHLASI
ALLAHUMMA AMEEEEEEEEEEEEEEEEN
NAMADINA BABAN MARYAM
yanayimuku Fatan An Tashi Lafiya
Dafatan Zamu yini Lafiya@
@@@@@@@@@@@@@@@ @

04/08/2015

Wani Mutumi ne ya fito daga Gidansa da Motarsa
mai kyau. Babu kudi a Aljihunsa Sai N2,000
kachal.
Yana cikin tafiya sai ya hadu da Check point. Sai
wani Mopol ya tareshi ya shiga gaban Motarsa
yace dole sai ya bada N2,000 Sannan zai wuce.
Shi kuma yana Sauri, yayi ta masa magiya akan
yayi haquri amma yaqi ya barshi. Haka dole ya
haqura ya bashi N2,000 ba don yana so ba.
Bayan ya wuce ya tafi har yayi nisa sai yaji Ringing
din waya a kusa dashi, yana dubawa sai yaga waya
'Samsung Galaxy s6' sai ya daga ya kara akunne
sai yaji ance "Nine Mopol din da muka hadu da kai
a Check Point yanxu, Na manta wayata ne akan
Kujerar Motarka, Dan Allah ka dawo ka bani wallahi
Jiya na siyo ta da dukkan Albashi na"
Wai idan kaine / kece Mai Motar xaka/zaki dawo
kuwa??

06/05/2015

ALLAHU AKBAR:
Comment & Share
Da wadannan falala guda 12 daga ingantattun
Hadissai na Manzon Allah S.A.W.
1. Annabi S.A.W. ya ce: "Wanda ya karanta
Qulhuwallahu Ahad sau 10 a jere, Allah zai gina
masa katafaren gida acikin Aljanna".
[Sahihul Jami'i. 6348]
2. Manzon Allah S.A.W. ya ce: "Wanda ya karanta
Ayatul Khursiyyu bayan kowace Sallah ta farilla,
babu abinda zai hanashi shiga aljanna saidai Idan
bai mutu ba. [Sahihul Jami'i]
3. Manzon Allah S.A.W. yache: "Idan mutum yazo
kwanchiyar barci a saman shimfidarsa, ya karanta
Qulya ayuhal kafirun, falalar yin hakan shine; Idan
mutum ya mutu a cikin daren, bazai mutu mushiriki
ba" [Sahihul Jami'i]
4. Manzon Allah S.A.W. Ya ce: "Wanda ya karanta
suratul khahfi ranar juma'a, Allah zai haskaka masa
da haske har zuwa wata juma'a yana chikin farin
ciki yana cikin jin dadi" [Sahihul jami'i]
5. Manzon Allah S.A.W. ya ce: "Wanda ya haddace
ayoyi goma na farkon suratul khahfi, Allah zai
tsareshi daga fitinar dujal" [Sahihul Jami'i]
6. Manzon Allah S.A.W. yache:
" wanda ya yi Alwalla ya kyautatata, bayan yagama
sai yace; Ash hadu anla'ilaha ilallah wahdahu
lasharikalahu, wa'anna Muhammadan Abduhu
warasulahu; Allahumma Ja'alna minattawwabina
waja'alna minal muta dhahirina. Za'a buda masa
qofofi na Aljanna guda 8 yazabi qofar da yakeso
yashiga" [Sahihul Jami'i]
7. Abdullahi Dan Umar Ya ce; wata rana mun
kasanche muna Sallah bayan Manzon Allah S.A.W.
da Annabi ya d**o daga ruku'u sai yace:
SAMI'ALLAHU LIMAN HAMIDAHU sai wani a cikin
sahabbai yace; RABBANA WALAKAL HAMDU
HAMDAN KHATHIRAN DAYYIBAN MUBARAKAN FIHI
MUBARAKAN ALAIHI K**A YUHIBBU RABUNNA
WAYARDA. da aka sallame sai Manzon Allah
S.A.W. ya waiwayo yace: wanene yafadi wannan
kalmar? sai Sahabin yace nine ya Rasulillah, sai
Annabi yace, na ga Mala'iku talatin da ya kai
sunata rige-rigen (Gaggawar) wazai rubuta wannan
aikin yakaima Allah (SWT)" [Bukhari]
8. Annabi S.A.W. ya ce: " wanda yayi Raka'a 12 ta
nafila tsakanin dare da rana Allah zai gina masa
gida a cikin gidan Aljanna" [Sahihul Jami'i]
9. Annabi S.A.W. ya ce wanda ya kiyaye, yanayin
Raka'a 4 ta nafila kafin Sallar Azahar dakuma
Raka'a hudu ta nafila bayan sallar Azahar Allah zai
haramta masa shiga wuta" [Sahihul Jami'i]
10. Annabi S.A.W. ya ce: "Allah ya jiqan wanda ya
yi Sallah Raka'a 4 kafin sallar la'asar" [Sahihul
Jam'i]
11. Annabi S.A.W. ya ce: "Wanda ya ke karanta
ayoyi 10 da dare baza'a sanyashi cikin gafalallu ba,
wanda ya ke karanta ayoyi 100 da dare za'a
rubutashi chikin (Qanitina) wato masu bauta ga
Allah, Wanda yake karanta ayoyi dubu kullum, za'a
rubutashi daga cikin masu arzikin lahira" [Sahihul
Jami'i]
12. Manzon Allah S.A.W. Ya ce: "mutum ya yi
Sallar Nafila inda babu wanda ke ganinsa (cikin
duhu), Allah zai linka masa lada sau 25 fiyeda kayi
agaban jama'a suna ganinka" [Sahihul Jami'i].
Allah yasa mu dace akan gaskiya yasa mu mutu
muna masu imani...
PLS TYPE Ameen.

25/04/2015

Assalamu alaikum warahmatullahi ta'ala wabara katuhu

sabahul khair my friends may almghty accept our congregational prayer and make our last word to be "la'aiaha illallah Muhammadarrasulullah swallallhu alaihi wasallam"

Ameen

Assalamu alaikum warahmatullahi ta'ala wabara katuhuSEEKING OF ALLAH FORGIVENESS******************************Oh Allah p...
21/04/2015

Assalamu alaikum warahmatullahi ta'ala wabara katuhu

SEEKING OF ALLAH FORGIVENESS
******************************
Oh Allah protect us from fitna in this life and grant us protection from the punishment of the grave

Ameen ya Allah

18/02/2015

SAKO DAGA ANNABI S.A.W
Manzo {SAW} yace " wani lokaci zaizo
wa al'ummata inda zasu so abubuwa biyar su manta
da wasu biyar.
1-Zasu so duniya su manta da lahira.
2-Zasu so gidaje su manta da kaburbura.
3-Zasu so dukiya amma su manta da
hisabi.
4-Zasu so Iyali su manta da haqqoqansu.
5-Zasu so ransu su manta da Allah.
To bani basu , suma basu bani."
Yan'uwa munfa shigo lokacin , gani yadda mutane
idanunsu sun rufe akan son
duniya, kuma lallai dayawan mutane ayyukansu
kawai zaka kalla kasan lahira
bata gabansu , k**ar basu da yaqini game da ita ,
yayin da wasu ke tafka
barna son ransu basu tuna Allah b***e ukubar da ya
tanadar , iyali kuwa anjibge
su ba'a cika musu haqqoqa , ga
rashin adalci a tsakaninsu , ya kake gameda
abubuwan da aka ambata ?
Allah yasa mu gyara.

17/02/2015

Assalam

Yan uwana musulmai

Mukiyaye harshenmu mudena anbaton yan uwa musulmai face akan alkhairi

Domin kuwa rashin kiyaye harshe ya jawa wasu mata guda biyu kusan halaka matannande bakomaine yajawo musu halakaba face gulma!

Su sun kasance watarana sunyi azimi da lokacin buda baki yayi sai akaga suna cikin wani mawuyacin hali na wata irin cuta kai harma maganar baki nagagararsu

Sai wani daga cikin danginsu yaje gun manzon allah(saw)kan cewa yaje yansu sai yace aa sai de akawosu

Bayan ankawosu sai yake sanarda mutanen kan cewa wayannan sunkasance magulmatane abunda yajawo musu wannan abun shine

Lokacin da ake buda sun zaunane kawai ba'abunda sukeyi face cin naman mutane wato(gulma)

Bayan yagama musu bayani sai ya dauki wata kwarya yabawa dayar yace tayi amai aikuwa tanayin amai saiga naman mutanene kawai take amarwa da ruwan gyambo hak**a dayar bayan sungama

sai yayi musu wa'azi sannan yasallamesu
Allah yakaremu

IMAM AHMAD yaruwaitoshi acikin musnad

Alhamdulillah

Address

Gombe State Near Jekadafari Way
Gombe
GOMBE

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Slave of ALLAH posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share