15/06/2026
DA ƊUMI-ƊUMI: Dr. Madinatu Dahiru Bauchi Ta Kafa Tarihi A Arewacin Najeriya
Dr. Madinatu Dahiru Usman Bauchi ta zama mace ta farko a Arewacin Najeriya da ta samu Digirin Digirgir (PhD) a fannin Fiqhu, wato Ilimin Shari'ar Musulunci.
Dr. Madinatu, 'ya ga marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi (RA), ta kammala karatunta ne a wata fitacciyar jami'ar Musulunci da ke ƙasar Morocco.
Baya ga wannan nasara, ita ma mahaddaciyar Alƙur'ani ce kuma ƙwararriya a fannoni daban-daban na ilimin Musulunci.
Nasararta ta zama abin alfahari da ƙarfafawa ga mata Musulmai a Najeriya da nahiyar Afrika baki ɗaya.
Wane fata za ku yi mata?