17/12/2023
NANA ZAINAB BINT JAHSH RA (1)
"زوجكن اهاليكن وزوجني الله تعالى من فوق سبع سموات"
NASABARTA DA AURENTA DA ANNABI (SAW)
Nana Zainab bint Jahsh رضى الله عنها وأرضاها ita ce, Zainab 'yar Jahsh dan Ri'bàb dan Ya'amur Al-Asadiyya. Mahaifiyarta ita ce: Umaimah bint Abdulmuddalib, gwaggon Annabi صلى الله عليه وسلم 'yar'uwar mahaifinsa, kuma 'yar'uwar Hamza bn Abdulmuddalib رضى الله عنه baffan Annabi صلى الله عليه وسلم. Saboda haka ita kanwa ce ga Annabi صلى الله عليه وسلم.
Nana Zainab matashiya ce kyakkyawa, 'yar madaukakin dangi na kuraishawa, jikar Abdulmuddalib kakan Annabi صلى الله عليه وسلم.
Mijinta na fari shi ne Zaid bn Harith رضى الله عنه. Annabi صلى الله عليه وسلم ya riki Zaid kamar dansa har ma ana kiransa Zaid bn Muhammad, har sai da Allah سبحانه وتعالى ya hana a danganta kowa in ba ga mahaifinsa ba, shi ne aka dawo ana kiransa da Zaid bn Harith.
Annabi صلى الله عليه وسلم yana matukar kaunar Zaid, har ma ana kiransa dan lelen Manzon Allah صلى الله عليه وسلم. Da Zaid ya isa aure sai Annabi صلى الله عليه وسلم ya aura masa kanwarsa Zainab bint Jahsh. Ya zauna da ita tsawon shekara guda, amma zaman nasu bai yi dadi ba saboda tana ganinta karkashin bawa duk da cewa Annabi صلى الله عليه وسلم ya 'yanta shi, ita kuma ga ta da nasaba madaukakiya ta kuraishawa. Zaid sai ya rika kai kararta wajen Annabi صلى الله عليه وسلم, shi kuwa yana lallashinsa yana fada masa cewa ya ji tsoron Allah ya rike matarsa.
Larabawa a lokacin jahiliyya sun yarda cewa idan mutum yana rikon wani a matsayin dansa, to haramun ne a kansa ya auri matar da ya saki domin a wurinsu kamar ya auri matar dan da ya haifa ne bayan ya sake ta.
To da yake Allah سبحانه وتعالى ya yi nufin rushe waccan al'ada ta jahiliyya dongane da ya'yan riko wadanda ba daidai suke da ya'yan cikin mutum ba sai ya sanar da Manzonsa cewa Zaid zai saki matarsa Zainab shi kuma zai aureta bisa umarnin Allah سبحانه وتعالى.
Da zama ya ki yiwuwa tsakanin Zaid da matarsa Zainab sai ya sake ta.
Anas رضى الله عنه ya