Markaz al-Sunnah Dabai

Markaz al-Sunnah Dabai Education research center

14/10/2025

Duk gaskiyar ka ba kowa bane zai yarda da Abinda ka faɗa ba

Manzon Allah yafi kowa gaskiya amma mushrikan Makka s**a ƙarya ta shi

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Yafi Kowa hankali s**a ce Mishi mahaukaci

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Yafi kowa imani s**a ce mishi boka ne shi

Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama Yafi kowa daɗin zance da iya magana s**a ce mishi mawaƙi ne shi.

Dukkan waɗannan Abubuwan basu rage Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da komai ba.

Haka dabi'ar waɗanda basa son gaskiya take dole a matsayin ka na da'eyah za'a yi maka sharri ƙarya dakuma ƙage.

Allah ta'ala ya gaskiya tayi nasara a ko yaushe

Babban M***i na ƙasar Saudiyya ya Rasu.Sheikh Abdul-Azeez Bin Abdullah Alu- Sheikh 𝗥𝗨𝗕𝗨𝗧𝗔𝗪𝗔: 𝗔𝗟𝗜𝗬𝗨 𝗡𝗔𝗦𝗜𝗥 𝗗𝗔𝗕𝗔𝗜 (𝑨𝑩𝑼-𝑲𝑯𝑨𝑳...
24/09/2025

Babban M***i na ƙasar Saudiyya ya Rasu.

Sheikh Abdul-Azeez Bin Abdullah Alu- Sheikh

𝗥𝗨𝗕𝗨𝗧𝗔𝗪𝗔: 𝗔𝗟𝗜𝗬𝗨 𝗡𝗔𝗦𝗜𝗥 𝗗𝗔𝗕𝗔𝗜 (𝑨𝑩𝑼-𝑲𝑯𝑨𝑳𝑰𝑫)

Sunan shi Abdul-Azeez ɗan Abdullahi ɗan Muhammad ɗan Abdullaɗif ɗan Abdurrahman ɗan Hasan ɗan Sheikh Muhammad bin Abdulwahab Mujaddadin musulunci. Akwai mutane Biyar tsakanin shi da Sheikh Ibin Abdulwahab me littafi kitabuttauhid. Sannan duk wanda kaga An kira da آل الشيخ toh zuri'ar Sheikh Muhammad bin Abdulwahab ne.

Sun fito daga ƙabilar Banu tamim, masu karatun tarihi sun san gudummawar su ga Musulunci da kyakkyawan yabo da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yayi musu.

An haife shi a Makkah 6-02-1362H wanda yayi dai-dai da 10-02-1943M Ranar Laraba

An haife shi yana da matsalar Gani da idon shi duk da a lokacin ba makaho bane amma ya makance gaba-daya yana ɗan shekara 19 a duniyar Bayan an yi Mishi Aikin ido a riyad.

Ya Haddace Alkur'ani yana ƙaramin Yaro sannan yayi karatu a wajen Malamai da dama daga cikin su akwai
1. Muhammad bin Ibrahim Alu-sheikh
2. Sheikh Abdul-Azeez Bin Baz
3. Sheikh Abdul-Azeez Bin Salih Al-Murshid
4. Sheikh Abdul-Azeez Ash-shasriy

Yana da Ƴaƴa 4
1. Abdullahi
2. Muhammad
3. Umar
4. Abdurrahman

Ayyuka da kuma gwagwarmayar Aiki da da'awa.

1. Ya Fara aiki na farko a matsayin Malamin jami'a shekara 60 da s**a gabata.

2. Ya zama babban limamin juma'a a masallacin Malamin shi kuma ɗan uwan kakan shi Muhammad Bin Ibrahim shekaru 48 da s**a gabata.

3. Associates professor ne shekaru 47 da s**a gabata

4. Limamin Arafah ne a masallacin Namirah daga 1402 zuwa 1436 tsawon shekaru 34 yana khudbah

5. Tsawon shekaru 40 dai-dai yana member na majalisar ƙoli ta Malaman Addini na Saudiyya daga baya yazama shugaban ta

6. Limamin masallacin Sheikh turkiy tun 1412 shekaru 35 kenan zuwa yau kuma akan wannan aikin ya rasu.

ya rasu jiya talata da Asuba
01-04-1447
23-09-2025

Allah ta'ala ya gafarta Mishi

14/07/2025
11/07/2025

Big shout out to my newest top fans! A Sani Dabai

Assalamu alaikum Wa rahmatullahi wa barakatuhu KAUYATA "YAN UWANTAKA A MUSULUNCI Tattaunawa da zata kasance tsakanin Dal...
17/01/2025

Assalamu alaikum Wa rahmatullahi wa barakatuhu

KAUYATA "YAN UWANTAKA A MUSULUNCI

Tattaunawa da zata kasance tsakanin Daliban Wannan Markaz al-Sunnah Dabai Gobe Asabar A Masallacin Alh. Ahmadu Danbiye Dabai Tsakanin Magrib Da Isha'i.

Allah ya bada Ikon Zuwa.

12/09/2024

Musulmi na iya zama halakakke ne kawai idan baya karatu Koh kuma Malami yake bi Ba hujja ba.

Babu yanda zaka tsira baka karatu Koh baka zuwa Wajen da ake karatu Koh kuma baka tambaya ta ilimi.

Haka nan duk ƙoƙarin ka Wajen Neman karatun addini da ziyartan majalisin karatu in har Malamin ka kawai kake saurare kuma baka yarda da kowa ba sai shi kuma ba Ruwan ka da hujjoji, abinda ya dame ka kawai shine me Malamin ka ya faɗa, Toh ka gama hallaka.

Koh me ahalari cewa yayi
ويسأل العلماء
ya tambayi Malamai, abinda ake so ka tambayi Malamai ba ka tambayi malami ba

Sannan littafin Allah cewa yayi
فسألوٱ أهل الذكر
Ku tambayi ma'abota sani (ilimi) shima kunga ba mutum daya akache

Aliyu Nasir Sambo-ja
Director Da'awah
Markaz Al-sunnah Dabai

09/07/2024



Assalamu Alaikum Warahmatullah





Goma ga watan Almuharram itache ranar Ashurah akwai muhimman abubuwa da tarihi ya kiyaye cewar sun faru a wannan ranar.

Amma dai wanda yafi taɓamu kai tsaye shine shahadar da jikan ma'aiki Sallallahu alaihi Wasallama kuma shugaban matasan aljannah yayi Al-imamu Husaini Radiyallahu Anhu a wannan ranar ta ashurah.

Koh shakka babu dukkanin ɗaukachin Ahlu-sunnah suna da fahimtar cewar An kashe sayyiduna Al-husain ne matsayin Wanda aka zalunta.

Sai dai Akwai bukatar mu fahimci wasu abubuwa guda goma 10 wanda dukkansu suna da alaƙa da shahadar sayyiduna Husaini Radiyallahu Anhu, kuma wanda ya jahilce su bai kamata ya tsoma baki akan qadiyyar ba.

1. Kafin Ya fita domin zuwa Wajen da yayi shahada yana ina ne da Zama ?

2. Shin Sahabbai da sauran Ahlul-baiti sun goyi bayan ya fita zuwa inda yayi shahada Koh sun tsawatar mishi akan haka. ?

3. Shin su wanene acikin tawagar shi lokacin da ya fita domin dai bashi kaɗai bane.

4. Menene sababbin fitar shi zuwa inda yayi shahada ? Sanin wannan yanada muhimmanci

5. Shin sayyiduna Husaini shi kaɗai ne yayi shahada Koh akwai wasu Tare Da shi awannan lokacin da suma s**a yi shahadar, amma dayawan musulmi basa jin sunan su

6. Su wanene s**a gayyato shi inda yayi wannan shahadar, shin sun taimaka mishi da ya iso Wajen, koh gadar zare su kayi mishi ?

7. Su wanene s**a kashe shi kuma ƙarƙashin jagorancin wanene

8. Menene matsayar Yazidu ɗan Mu'awiyah akan wannan mas'alar awajen sauran Musulmi

9. Shin wace wasiyya sayyiduna Husaini yayi ma ƴar-uwar shi zainab kafin yayi shahada, shin Mabiya addinin shi'ah suna kula da wannan wasiyyar Koh kuwa ?

10. Menene tarihin masu zanga-zanga da kuka da shiga Bala'i a dukkanin lokacin da irin wannan rana ta zagayo, wadda al'imam Husaini yayi shahada ?

Mu hadu a rubutun da suke biye domin yin ƙarin haske akan wannan in Sha Allahu

Engr Aliyu Nasir Sambo-ja

Address

Danja

Telephone

+2347030940471

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Markaz al-Sunnah Dabai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Place Of Worship

Send a message to Markaz al-Sunnah Dabai:

Share