10/04/2026
*TUNATARWARMU TA YAU*
*ABUBUWAN DA SUKE HAIFAR DA DAMUWA!*
Ibnul Qayyim R.A yace: “Qunci da Damuwa da Baqinciki suna samuwa ne ta 6angarori guda biyu: Na farko kwadayi da son duniya, Na biyu kuma taqaitawa wajan ayyukan da'a da biyayya”.
Wannan magana ta Ibnul Qayyim (Rahimahullah), tana ɗauke da zurfin hikima matuka, domin tana bayyana tushen damuwa daga bangaren zuciya da halayyar mutum.
-
1. Kwadayi da son duniya: Idan zuciyar mutum ta cika da son duniya fiye da kima misali, son kudi, son matsayi, son mulki, ko son yabo sai ya shiga cikin damuwa ta hanyoyi da dama. Ba ya gamsuwa: Duk abin da ya samu bai ishe shi ba, kullum yana neman ƙari.
-
Tsoron mutum ya rasa abin da yake da shi: Idan ya samu wani abu, sai ya fara tsoron kada ya rasa shi. Kwatanta kansa da wasu: Yana kallon abin da wasu suke da shi, sai ya ji kamar shi bai kai ba. Gasa marar iyaka: Rayuwa ta koma kamar tseren da ba shi da ƙarshe.
-
A nan ne damuwa ke shiga zuciya, domin duniya ba ta taɓa cika burin mutum gaba ɗaya ba.
-
Sabida haka, maganin wannan shi ne: qana'a (yarda da abin da Allah Ya raba) da kuma tuna cewa dukkanin Abubuwan da ke cikin duniya masu karewa ne, in Mutum ya fahimci haka to hakika ya huta, In Sha Allah .
2. Taqaitawa a kan ayyukan da'a da biyayya: Bangare na biyu shi ne sakaci wajen ibada da kusanci ga Allah. Idan mutum ya yi sakaci. Zuciya tana bushewa: Ba ta samun natsuwa da haske. Rashin jin dadi a zuciya: Ko da yana da dukiya, ba ya jin farin ciki na hakika, kullum yana cikin kunci da damuwa. Sabida ya rasa abin da ke ciyar da zuciyasa.
Allah (SWT) Ya ce: "Lalle da ambaton Allah ne zukata suke samun natsuwa." (Suratul Ra’d: 28).
Idan aka bar zikiri, sallah, karatun Al-Qur’ani, da sauran ibadu, zuciya tana shiga cikin duhu da damuwa.
Saboda haka, hanya mafi kyau ita ce a rage yawan haɗa zuciya da duniya, a kuma ƙara kusanci da Allah. Idan mutum ya kasance mai qana’a da kuma yawaita ibada, zai samu nutsuwa da farin ciki na gaskiya a rayuwarsa.