26/05/2026
ZIKIRIN SAFE DA MARAICE
اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ خَلَقْتَنِي، وَأَنَا عَبْدُكَ,وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ, أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ لَكَ بِذَنْبِي فَاغْفِرْ لِي فَإِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ
Shugaban Dukan Istigfári:
“Alláhumma anta Rabbí, lá’iláha illáh anta, halaqtaní, wa aná abduka, wa ana alá wa’adika mastada’atu. A’úzu bika min sharri má sana’atu, wa abú’u bika bi ni’imatika alayya, wa abú’u laka bi zambí, fagfir lí fa’innahú lá yagfiruz-zunúba illá anta.”
(Ya Ubangiji! Kai ne abin bautata, babu wani abin bauta da gaskiya sai kai. Kai ka halicce ni; ni bawanka ne, ina kuma nan a kan alkaawari da yarjejeniyar da take tsakanina da kai gwargwadon ikona. Ina neman tsarinka daga sharrin abin da na aikata. Ina godiya a kan ni’imar da ka yi mani, ina kuma yi maka ikirarin ayyuka na na zunubi tare da rokon ka yi mani gafara, domin babu wanda yake gafarta zunubai sai kai.)
Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Duk wanda ya karanta wannan addu’a da rana, yana mai cikakken imani da ita. Idan Allah ya karbi rayuwarsa a wannan rana, kafin maraice, to, ko shakka babu yana daga cikin ‘yan Aljanna.
Wanda duk kuma ya karanta ta a cikin dare, yana mai cikakken imani da ita. Idan Allah ya karbi rayuwarsa kafin a wayi gari, to, yana daga cikin ‘yan Aljanna.” (Buhari:6306).
JNI MEDIA RISHI ✍️