Masallaci Juma'a Jama'atu Nasral Islam Rishi

Masallaci Juma'a Jama'atu Nasral Islam Rishi Alhamdulillah! Barka Da Zuwa Shafin Yada Alkhairi Da Karatuttukan Malaman Musulumci Musamman Na JNI Rishi. Allah Yasa Mu Amfana Kuma Mu Amfanar 👏

CIKIN HOTUNA:Yadda Aka Gudanar Da Sallar IDI A Masallaci IDI Na Garin RISHI Wanda Mal. Mu'azu Saleh Imam Ya Jagoranta.Al...
27/05/2026

CIKIN HOTUNA:

Yadda Aka Gudanar Da Sallar IDI A Masallaci IDI Na Garin RISHI
Wanda Mal. Mu'azu Saleh Imam Ya Jagoranta.

Allah Ya Karba Mana Ibadunmu
Allah Ya Maimaita Mana👏

JNI MEDIA RISHI ✍️

27/05/2026

Kai Tsaye Daga MASALLACI IDI

26/05/2026

SANARWA 📢

IDAN ALLAH YA KAIMU GOBE,
ZA'A TSAIDA SALLAR IDI BABBA DA MISALIN QARFE 8:45 NA SAFIYA.

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ خَلَقْتَنِي، وَأَنَا عَبْدُكَ,وَأَنَا عَلَى عَ...
26/05/2026

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE

اللَّهُمَّ أَنْتَ رَبِّي لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ خَلَقْتَنِي، وَأَنَا عَبْدُكَ,وَأَنَا عَلَى عَهْدِكَ وَوَعْدِكَ مَا اسْتَطَعْتُ، أَعُوذُ بِكَ مِنْ شَرِّ مَا صَنَعْتُ, أَبُوءُ لَكَ بِنِعْمَتِكَ عَلَيَّ، وَأَبُوءُ لَكَ بِذَنْبِي فَاغْفِرْ لِي فَإِنَّهُ لَا يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلَّا أَنْتَ

Shugaban Dukan Istigfári:

“Alláhumma anta Rabbí, lá’iláha illáh anta, halaqtaní, wa aná abduka, wa ana alá wa’adika mastada’atu. A’úzu bika min sharri má sana’atu, wa abú’u bika bi ni’imatika alayya, wa abú’u laka bi zambí, fagfir lí fa’innahú lá yagfiruz-zunúba illá anta.”

(Ya Ubangiji! Kai ne abin bautata, babu wani abin bauta da gaskiya sai kai. Kai ka halicce ni; ni bawanka ne, ina kuma nan a kan alkaawari da yarjejeniyar da take tsakanina da kai gwargwadon ikona. Ina neman tsarinka daga sharrin abin da na aikata. Ina godiya a kan ni’imar da ka yi mani, ina kuma yi maka ikirarin ayyuka na na zunubi tare da rokon ka yi mani gafara, domin babu wanda yake gafarta zunubai sai kai.)

Annabi sallallahu alaihi wa sallam ya ce: “Duk wanda ya karanta wannan addu’a da rana, yana mai cikakken imani da ita. Idan Allah ya karbi rayuwarsa a wannan rana, kafin maraice, to, ko shakka babu yana daga cikin ‘yan Aljanna.

Wanda duk kuma ya karanta ta a cikin dare, yana mai cikakken imani da ita. Idan Allah ya karbi rayuwarsa kafin a wayi gari, to, yana daga cikin ‘yan Aljanna.” (Buhari:6306).

JNI MEDIA RISHI ✍️

GOBE AZUMIN ARFA...Yakai Dan'uwa kayi kokarin Yin Azumin Arfa kasaka Iyalanka Da Dukkan Wanda kake Da Iko Dashi.Muna Roƙ...
25/05/2026

GOBE AZUMIN ARFA...

Yakai Dan'uwa kayi kokarin Yin Azumin Arfa kasaka Iyalanka Da Dukkan Wanda kake Da Iko Dashi.

Muna Roƙon Allah Yasa Muna Daga Cikin Bayin Da Za'a Hafatar Musu Acikin Wannan Wata Mai Tarin Albarka Da Falala 🤲

JNI MEDIA RISHI ✍️

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE An samo daga Anas (RA) lallai annabi (saw) ya ce: "Duk wanda ya fada a lokacin da ya wayi gari, ...
24/05/2026

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE

An samo daga Anas (RA) lallai annabi (saw) ya ce: "Duk wanda ya fada a lokacin da ya wayi gari, ko a lokacin da ya yi yammaci:

«اللَّهُمَّ إِنِّي أَصْبَحْتُ أُشْهِدُكَ وَأُشْهِدُ حَمَلَةَ عَرْشِكَ وَمَلَائِكَتَكَ، وَجَمِيعَ خَـــلْقِكَ أَنَّـــكَ أَنْـــــــــــــتَ اللَّهُ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ، وَأَنَّ مُحَمَّدًا عَبْدُكَ وَرَسُولُك».

Ma'ana: "Ya Allah lallai ni na wayi gari ina shaida maka, kuma ina shaida ma mala'ikun da su ke dauke da al'arshinka, da mala'ikunka, da sauran halittunka gabadaya cewa: Lallai kai ne Allah wanda babu abun bauta da gaskiya sai kai, kuma lallai Muhammadu bawanka ne kuma manzonka ne". Wanda ya fadi haka Allah zai yanta daya bisa hudunsa (1/4) daga wuta, Wanda kuma ya fade shi sau biyu Allah zai yanta rabinsa ne, wanda kuma ya fada sau uku to shi kuma Allah zai yanta uku bias hudunsa (3/4) daga wuta, In kuma ya fade shi sau hudu to Allah zai yanta shi gabadayansa daga wuta".

Abu-dawud ya rawaito shi da isnadi mai kyau (hasan). Da An-nasa'iy a cikin littafinsa "amalul yaumi wallailah", da Isnadi hasan, Lafazinsa kuma shi ne:

«مَنْ قَالَ حِينَ يُصْبِحُ: اللَّهُمَّ إِنِّي أَصْبَحْتُ أُشْهِدُكَ وَأُشْهِدُ حَمَلَةَ عَرْشِكَ، وَمَلَائِكَتَكَ وَجَمِيعَ خَــــلْقِكَ، أَنَّــكَ أَنْتَ اللَّهُ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنْتَ، وَحْدَكَ لَا شَرِيكَ لَكَ، وَأَنَّ مُحَمَّدًا عَبْدُكَ وَرَسُولُكَ، أَعْتَقَ اللَّهُ رُبُعَهُ ذَلِكَ الْيَوْمَ مِــــــنَ النَّارِ، فَإِنْ قَالَ أَرْبَعَ مَرَّاتٍ أَعْتَقَهُ اللَّهُ ذَلِكَ الْيَوْمَ مِنَ النَّارِ».

Ma'ana: "Duk wanda ya fada a lokacin da ya wayi gari: Ya Allah lallai ni na wayi gari ina shaida maka, kuma ina shaida ma mala'ikun da su ke dauke da al'arshinka, da mala'ikunka, da sauran halittunka gabadaya cewa: Lallai kai ne Allah wanda babu abun bauta da gaskiya sai kai; kai daya ka ke baka da abokin tarayya. kuma lallai Muhammadu bawanka ne kuma manzonka. = Allah zai yanta daya bisa hudunsa (1/4) a wannan yinin daga wuta, In kuma ya fade shi sau hudu to Allah zai yanta shi a Wannan Wuni Gaba Dayanshi Daga Wuta.

JNI MEDIA RISHI ✍️

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهُوَ عَل...
20/05/2026

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE

لاَ إِلَهَ إِلاَّ اللَّهُ وَحْدَهُ لاَ شَرِيكَ لَهُ، لَهُ الْمُلْكُ وَلَهُ الْحَمْدُ، وَهُوَ عَلَى كُلِّ شَيْءٍ قَـدِيرٌ.

La ilaha illal-lahu wahdahu la shareeka lah, lahul-mulk, walahul-hamd, wahuwa AAala kulli shayin qadeer.(10)

Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kadai, babu abokin tarayya a gare Shi. Mulki nasa ne shi kadai, yabo ma nasa ne shi kadai, kuma Shi mai iko ne bisa komai.

(Sau Goma, ko Sau Daya, Idan Anji kasala).

Allah Yasa Mudace Duniya Da Lahira 👏

JNI MEDIA RISHI ✍️

MUGUN IDO YAFI HATSARI FIYE DA SIHIRI!Wajibi ne musulmi ya kiyaye kansa daga shedanun aljanu da mutane, ta hanyar dogaro...
19/05/2026

MUGUN IDO YAFI HATSARI FIYE DA SIHIRI!

Wajibi ne musulmi ya kiyaye kansa daga shedanun aljanu da mutane, ta hanyar dogaro da Allah da tawakkali da neman tsarinsa da rokonsa, da karanta addu'o'in neman tsari da aka ruwaito daga Annabi (SAW).

KU RINKA KARANTA:

"Hasbi Allahu la ilaha illa huwa, 'alayhi tawakkaltu wa huwa Rabb ul-'arsh il-'azeem.

(Allah Ya ishe ni. La ilaha illa Huwa (Babu abin bautawa da gaskiya sai Shi) a gare Shi na dogara, kuma Shi ne Ubangijin Al'arshi mabuwayi). Kafa 10 ko abinda ya sauwaka.

JNI MEDIA RISHI ✍️

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE أَصْـبَحْنا علـى فِطْـرَةِ الإسْلام ، وَعَلـى كَلِـمَةِ الإخْـلاص، وَعلـى دينِ نَبِـيِّنا مُحَمَ...
19/05/2026

ZIKIRIN SAFE DA MARAICE

أَصْـبَحْنا علـى فِطْـرَةِ الإسْلام ، وَعَلـى كَلِـمَةِ الإخْـلاص، وَعلـى دينِ نَبِـيِّنا مُحَمَّدٍ  وَعَلَى مِلَّةِ أَبِينَا إِبْرَاهِيمَ حَنِيفًا مُسْلِمًا وَمَا كَانَ مِنَ الْمُشْرِكِينَ.

Asbahna 'ala fitratil-islam, wa’ala kalimatil-ikhlas, waAAala deeni nabiyyina Muhammad  wa'ala millati abeena Ibraheem, haneefan musliman wama kana minal-mushrikeen.

Mun wayi gari a kan kiran da Allah ya yi mana ta Musulunci, kuma a kan addinin Annabinmu Muhammadu, tsira da aminci su tabbata a gare shi, kuma a kan addinin Babanmu Ibrahim, mai mikewa zuwa ga addinin gaskiya, Musulmi, bai kasance daga cikin mushrikai ba.

JNI MEDIA RISHI ✍️

FALALAR KWANAKI GOMA NA FARKON ZUL-HIJJI TARE DA MAL. LAWAL MUHAMMAD.Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijjah Na Daga Cik...
18/05/2026

FALALAR KWANAKI GOMA NA FARKON ZUL-HIJJI TARE DA MAL. LAWAL MUHAMMAD.

Kwanaki Goma Na Farkon Watan Zul-Hijjah Na Daga Cikin Mafiya Daraja A Musulunci.
Allah Ya Fifita Su Da Ibada, Lada Da kuma kusanci Zuwa Gare shi.
Waɗannan kwanaki dama ce Ga Mumini Wajen ƙara Ayyukan Alheri kamar Azumi, Zikiri, Sadaka, Sallah Da Tuba.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce:
وَٱلْفَجْرِ • وَلَيَالٍ عَشْرٍ
“Ina Rantsuwa Da Alfijir.
Da kuma Dare Goma.”
Suratul Fajr: 1–2

Mafi Yawan Malamai kamar Abdullah Ibn Abbas Sun Bayyana Cewa “Dare Goma” ɗin Nan Sune kwanaki Goma Na farkon Zul-Hijjah.

Haka kuma Allah Ya ce:
وَيَذْكُرُوا۟ ٱسْمَ ٱللَّهِ فِىٓ أَيَّامٍ مَّعْلُومَٰت
“Domin Su Ambaci Sunan Allah A Wasu kwanaki Sanannu.”Suratul Hajj: 28

Abdullah Ibn Abbas Yace: “Kwanaki sanannu” Sune kwanaki Goma Na Zul-Hijjah.

FALALAR WADANNAN KWANAKI:

Abdullahi Dan Abbas R.A Yace: Manzon Allah ﷺ ya ce:
“Babu Wasu kwanaki Da Aiki Na Gari Yafi Soyuwa Ga Allah kamar waɗannan kwanaki goma.Sai Sahabbai s**a ce: “Ko jihadi a tafarkin Allah?” Sai ya ce: “Ko jihadi ma bai kai ba, sai mutumin daya Fita Da Ransa Da Dukiyarsa Bai Dawo Da komai ba.
”Bukhari Ne Ya Ruwaito.
-
Yan uwa Musulmi, Waɗannan kwanaki Basa Zuwa Sau Biyu (2) A Shekara, Kada ka bari su wuce ba tare da ka tara Ayyukan Alheri ba, watakila Wannan Shine Damar Da Zata Zama Sanadin Gafarar Allah Da Shiga Aljannah.

Allah Yasa Mudace Da Amfani Da kwanaki Goma Na Zhul Hajji Cikin Ibada Da Ikhlasi.

JNI MEDIA RISHI ✍️

Address

Along District Head Palace
Bauchi

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Masallaci Juma'a Jama'atu Nasral Islam Rishi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share