ECWA Church Anglo-Jos, Plateau State

ECWA Church Anglo-Jos, Plateau State Welcome to the official page of ECWA Anglo-Jos. Follow us for Bible teachings, Church events, Sermons and fellowship. God bless you!

ECWA Elects General Secretary and Vice President at 73rd General Council MeetingThe Evangelical Church Winning All (ECWA...
22/04/2026

ECWA Elects General Secretary and Vice President at 73rd General Council Meeting

The Evangelical Church Winning All (ECWA) during the ongoing General Church Council has successfully conducted elections for the offices of General Secretary and Vice President, held at the ECWA International Conference Center in Jos, Plateau State.
Rev. Dr. Ayuba Asheshe was re-elected the ECWA General Secretary, while, Rev. Chidi Joseph Nmadubuko was elected ECWA Vice President and Rev. Dr. Ezekiel Babatunde Omidiji was elected as the new Trustee representing Zone 9
The Council, which brings together church leaders, delegates, and representatives from all ECWA districts and zones across Nigeria and beyond, serves as the highest decision-making body of the denomination. This year’s gathering, which began with opening prayers and a review of the church’s mission progress, featured elections as a key item on the agenda.

General Secretary Re-elected for Second Term

In a vote of confidence in his leadership, Rev. Dr. Ayuba Asheshe was re-elected as ECWA General Secretary for a second term.
His re-election reflects the Council’s approval of his stewardship during his first tenure, during which he oversaw administrative reforms and expanded outreach initiatives. Dr. Asheshe will continue to serve as the chief administrative officer of the church.

New Vice President Emerges

The race for the Vice President position was conducted in a peaceful and orderly environment. Rev. Chidi Joseph Nmadubuko emerged victorious after securing 220 votes.
Rev. Nmadubuko brings a wealth of pastoral and leadership experience to the role, and will work closely with the ECWA President in providing strategic direction for the church.

Trustee Election for Zone 9

In another development, Rev. Dr. Ezekiel Babatunde Omidiji was returned elected as Trustee for Zone 9. His re-election ensures continuity in the management of ECWA’s trust properties and legal matters within the zone.

Prayer and Dedication

The atmosphere at the Conference Center was one of solemnity and gratitude. Delegates offered prayers for the newly elected officers, asking for divine wisdom, strength, and unity as they lead ECWA in the coming years.

We pray that God grants the General Secretary and the new Vice President wisdom to lead ECWA for His glory. Amen.

E-signed.
Danjuma Dickson Auta
ECWA PRO Unit.

21/04/2026

ABINCIN YININ ECWA
TALATA, 21 GA AFRILU 2026
NASSI: MAHUKUNTA 13:17-25
KAN MAGANA BAYYANUWAR UBANGIJI

MAHUKUNTA 13:17-25

17:Manowa ya ce, “Ka faɗa mana sunanka domin lokacin da maganarka ta cika mu girmama ka.”

18:Mala'ikan Ubangiji ya ce masa, “Don me kake tambayar sunana? Sunana asiri ne.”

19:Manowa kuwa ya yanka ɗan akuya, ya kuma kawo hadayar gāri, ya miƙa a kan dutse ga Ubangiji, mala'ika kuma ya yi al'ajabi. Manowa da matarsa s**a yi kallo.

20:Sa'ad da harshen wutar ya hau zuwa samaniya daga bagaden, sai mala'ikan Ubangiji ya hau zuwa sama ta cikin harshen wutar bagaden. Manowa da matarsa sun gani, s**a fāɗi a fuskokinsu a ƙasa.

21:Mala'ikan Ubangiji bai sāke bayyana ga Manowa da matarsa ba. Manowa kuma ya gane mala'ikan Ubangiji ne.

22:Manowa ya ce wa matarsa, “Ba shakka za mu mutu gama mun ga Ubangiji!”

23:Amma matarsa ta ce masa, “Da Ubangiji yana so ya kashe mu, ai, da bai karɓi hadayar ƙonawa da hadayar gārinmu ba, da kuma bai nuna mana, ko ya faɗa mana waɗannan abubuwa ba.”

24:Matar kuwa ta haifi ɗa, aka raɗa masa suna Samson. Yaron ya yi girma, Ubangiji ya sa masa albarka.

25:Ruhun Ubangiji ya fara iza shi, sa'ad da yake a zangon Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.

BAYYANUWAR UBANGIJI

Manowa ba zai daina cigaba da yin ƙarin tambayoyi ba yayin da yake ƙara yin bincike, yana ƙoƙarin fahimtar ko wanene wannan mala'ika mai ban mamaki a cikin surar mutum.

Zuciyarsa ta sa shi tambaya, "Ya sunanka, domin mu girmama ka sa'ad da maganarka ta cika?" (aya 17).

Martanin mala'ikan ya mayar mai nuna cewa shi ba mutum ba ne ko mala'ika domin sunansa "ya fi gaban fahimta" (aya 18).

Lokacin da Ubangiji ya sadu da Musa kuma ya ba shi umarni ya ceci mutanensa Ibraniyawa daga bauta a Masar, ya bayyanawa Musa cewa sunansa “Ni ne wanda ni ke” (Fitowa 3:14).

Wannan furci ya bayyana madawwamiyar dabi’ar Allah ta wanzuwar kansa da kasancewarsa marar canzawa.

Amsar Manowa ga wannan batu mai ban mamaki ita ce miƙa hadayar ƙonawa ta ɗan akuya da hatsi.

Sak**akon ya ba su mamaki domin mala’ikan Ubangiji ya bace tare da hayakin hadayar ta ƙonawa.

Tsoro da razana sun mamaye Manowa sa’ad da ya gane cewa Allah ya bayyana gare shi a cikin surar mutum, kuma an gaskata cewa babu wanda zai iya ganin Allah ya rayu.

Ka yabi Allah domin ma iya ganinsa ta wurin Yesu Almasihu, wanda ya zama “Emmanuel” namu, kuma ba za mu mutu ba.

Manowa da matarsa sun tsira da ganin Allah domin ya bayyana gare su a cikin surar mutum.

TAMBAYA: Allah yana tare da mu ta wurin Yesu Almasihu, amma ka sadu da shi a matsayin Ubangijinka da Mai Ceto?

ADDU’A: Yi anfani da amsarka ga tambayar da ke sama a matsayin jagorar addu’ar da za ka yi.

19/04/2026

ABINCIN YININ ECWA
LITININ, 20 GA AFRILU 2026
NASSI: MAHUKUNTA 13:8-16
KAN MAGANA: BI UMARNIN ALLAH

MAHUKUNTA 13:8-16

8:Sa'an nan Manowa ya yi roƙo ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangijina, ina roƙonka ka bar mutumin Allah wanda ka aiko, ya sāke zuwa wurinmu, ya faɗa mana abin da za mu yi wa yaron da za a haifa.”

9:Allah kuwa ya ji roƙon Manowa, ya sāke aiko da mala'ikansa wurin matar, sa'ad da take a saura, mijinta kuwa ba ya tare da ita.

10:Don haka sai ta sheƙa a guje zuwa wurin mijinta, ta faɗa masa, “Ga mutumin da ya zo wurina ran nan, ya sāke zuwa.”

11:Manowa fa ya tashi ya tafi tare da ita. Da ya zo wurin mutumin, sai ya tambaye shi, “Kai ne mutumin da ya yi magana da macen nan?” Sai ya amsa ya ce, “Ni ne.”

12:Manowa kuma ya ce, “Lokacin da maganarka ta cika, wane irin yaro ne zai zama, me kuma za mu yi?”

13:Mala'ikan Ubangiji ya amsa, ya ce wa Manowa, “Sai matarka ta kiyaye dukan abin da na faɗa mata.

14:Kada ta ci kowane irin abu da aka yi da inabi, kada kuma ta sha ruwan inabi ko abin sa maye. Kada ta ci haramtaccen abu, amma ta kiyaye dukan abin da na umarce ta.”

15:Manowa dai bai san mala'ikan Ubangiji ne ba, sai ya ce wa mala'ikan, “Ina roƙonka ka jira, mu yanka maka ɗan akuya.”

16:Amma mala'ikan ya ce masa, “Ko na jira ba zan ci abincinku ba, amma idan kana so ka yanka, sai ka shirya hadayar ƙonawa, ka miƙa ta ga Ubangiji.”

BI UMARNIN ALLAH

Manowa, mahaifin Samson, ya nemi ƙarin haske daga wurin Ubangiji game da saƙon da kuma juna biyu na matarsa.

Kalamansa kuma na darajantawa, yace "Ya Ubangiji, ka gafartawa bawanka... ka koya mana yadda za mu yi renon yaron" (aya 9), ya nuna bangaskiyarsa ga annabcin.

Da farinciki ya tambayi mala'ikan yadda zai yi wa ɗansa jagora. "Mala'ikan Ubangiji" sau da yawa yana wakiltar bayyanar da Yesu ya kasance da ita kafin ya zo cikin jiki.

Allah yana bada umarni don tallafawa waɗanda ya kira.

TAMBAYA:
Wanne umurni Allah ya ba ka don aikinka?

ADDU'A:
Yi addu'a bisa amsar tambayar da ke sama.

19/04/2026

Memory verse from children's ministry of ECWA Church Anglo-Jos, Plateau State during end of Bukuru DDC children's week of prayer

19/04/2026

Great performance by children ministry of ECWA Church Anglo-Jos, Plateau State at the end of Bukuru DDC children's week of prayer 19/04/2026

19/04/2026

ECWA Bukuru DCC end of children week of prayer Church Anglo-Jos, Plateau State 19/04/2026

18/04/2026

A rushed vow can bring irreversible sorrow.

18/04/2026

ABINCIN YININ ECWA
ASABAR, 18 GA AFRILU 2026
NASSI: MAHUKUNTA 12:1-7
KAN MAGANA: IFRAIMU YA KI YA TAIMAKAWA YEFTA

MAHUKUNTA 12:1-7

1:Mutanen Ifraimu s**a yi gangami s**a haye zuwa Zafon da shirin yaƙi. S**a ce wa Yefta, “Me ya sa ka haye zuwa yaƙi da Ammonawa, amma ba ka kira mu mu tafi tare da kai ba? To, yanzu za mu ƙone ka da gidanka.”

2:Amma Yefta ya amsa musu, ya ce, “Ni da mutanena mun yi ta jayayya da Ammonawa, na kira ku don ku cece ni, amma ba ku cece ni daga hannunsu ba.

3:Sa'ad da na ga ba ku cece ni ba, sai na yi kasai da raina, na haye don in yi karo da Ammonawa. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna. Me ya sa kuka zo yau don ku yi yaƙi da ni?”

4:Sa'an nan Yefta ya tara dukan mutanen Gileyad, s**a yi yaƙi da mutanen Ifraimu, s**a ci su. Mutanen Ifraimu s**a ce musu, “Ku mutanen Gileyad masu neman mafaka ne a cikin Ifraimu da Manassa!”

5:Mutanen Gileyad s**a hana mutanen Ifraimu hayewa ta mashigan Kogin Urdun. Idan wani mutumin Ifraimu gujajje ya ce, “Ku bar ni in haye.” Sai mutanen Gileyad su tambaye shi, “Kai mutumin Ifraimu ne?” Idan ya ce, “A'a,”

6:sai su ce masa, to, ka ce, “Shibbolet,” sai mutum ya ce, “Sibbolet,” gama ba ya iya faɗa daidai. Sai su k**a shi su kashe a mashigan Urdun. Mutanen Ifraimu da aka kashe a lokacin su dubu arba'in da dubu biyu (42,000) ne.

7:Yefta mutumin Gileyad ya shugabanci Isra'ilawa shekara shida, sa'an nan ya rasu. Aka binne shi a garinsu, wato Gileyad.

IFRAIMU YA KI YA TAIMAKAWA YEFTA

Ammonawa sun tsanantawa Gileyad shekaru da yawa, kuma lokacin da s**a nemi taimako ba su samu ba daga Ifraimu (aya 2-3).

Yefta bai bayyana dalilin da yasa s**a ki ba, amma bayan nasarar Gileyad, Ifraimu ta fuskance shi da kishi, kuma tana barazana ta yin lahani.

Wannan ya ta da tambayar: Ifraimu tana son Yefta ya kasa?

Lokacin da wani dangi ko shugaban kungiyarku ya ki bayar da hadin kai, nemi hikimar Allah don magance matsalar.

Halin Ifraimu ya haifar da rikici wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane 42,000.

TAMBAYA:
Shin za ka zabi ka kasance mai goyon bayan kungiyar ka?

ADDU'A:
Ya Allah, ka taimake ni in goyi bayan membobin kungiya ta da shugabanni yayin bada amsa mai ma'ana, cikin sunan Yesu. Amin.

17/04/2026

ABINCIN YININ ECWA
JUMA'A, 17 GA AFRILU, 2026
*NASSI: MAHUKUNTA 11:28-40
*KAN MAGANA: ALKAWARIN YEFTA GA UBANGIJI*

*MAHUKUNTA 11:28-40*

28:Amma Sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika masa ba.

29:Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko wa Yefta, sai ya tashi ratsa Gileyad da Manassa zuwa Mizfa ta Gileyad, daga can ya haura zuwa wurin Ammonawa.

30:Yefta kuwa ya yi wa'adi ga Ubangiji, ya ce, “Idan dai ka ba da Ammonawa a hannuna,

31:duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don ya tarye ni, sa'ad da na komo daga yaƙin Ammonawa da nasara, zai zama na Ubangiji, zan kuwa miƙa shi hadaya ta ƙonawa.”

32:Yefta ya haye zuwa wurin Ammonawa domin ya yi yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannunsa.

33:Ya karkashe su da mummunan kisa tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-keramim. Ya cinye biranensu guda ashirin. Da haka Ammonawa s**a sha kāshi a hannun Isra'ilawa.

34:Da Yefta ya koma gidansa a Mizfa, sai ga 'yarsa, tilo ta fito da kiɗa da rawa don ta tarye shi. Ita ce kaɗai 'yarsa, banda ita ba shi da ɗa ko 'ya.

35:Sa'ad da ya gan ta sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Kaito, 'yata, kin karya mini gwiwa, kin zamar mini babban dalilin wahala. Na riga na yi wa'adi ga Ubangiji, ba kuwa zan iya warware shi ba.”

36:Sai ta ce masa, “Baba, idan ka riga ka yi wa'adi ga Ubangiji, sai ka yi da ni bisa ga wa'adinka, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa, abokan gābanka.”

37:Ta kuma ce masa, “Ina so ka yardar mini in tafi kan duwatsu ni da ƙawayena in yi makokin budurcina har wata biyu.”

38:Sai ya ce mata, “Tafi.” Ya sallame ta, ta tafi har wata biyu ɗin. Ita da ƙawayenta kuwa s**a yi makokin budurcinta a kan duwatsu.

39:Bayan wata biyu, sai ta koma wurin mahaifinta, shi kuwa ya yi abin da ya yi wa Ubangiji wa'adi. Ta rasu ba ta taɓa sanin namiji ba. Wannan kuwa ya zama al'ada a cikin Isra'ila,

40:wato matan Isra'ilawa s**an fita kowace shekara su yi makoki kwana huɗu don 'yar Yefta, mutumin Gileyad.

ALKAWARIN YEFTA GA UBANGIJI

Sarkin Ammonawa ya ki amincewa da sakon Yefta kuma ya shirya yakai wa Isra'ila hari.

Lokacin Ruhun Ubangiji ya sauko bisa Yefta, domin yin yaki da Ammonawa.

Ya yi alkawari: "Idan ka bada Ammonawa a hannuna, duk abinda ya fito daga cikin gida don ya tarbe ni zai zama na Ubangiji, ni kuma zan miƙa shi hadaya ta konawa." (aya ta 31).

Yefta bai da bukatar yin irin wannan alkawarin, amma ya cika, yarsa ta karfafa shi, wadda ta bada kanta don sadaukarwa.

Masana sun yi muhawara game da ainihin abinda ya faru, amma aya ta 39 ta nuna cewa ta yi hidimar Allah dukan kwanakin ranta a maimakon ta yi aure.

Wannan yana nuna muhimmancin yin la'akari da alkawura a hankali saboda irin sak**akon da hakan zai iya haifarwa.

TAMBAYA: Shin koyaushe kana cika alkawuranka da aminci?

ADDU'A:Ya Allah, ka ba ni hikimar yin tunani da kyau kafin in yi wani alkawari, cikin sunan Yesu. Amin.

16/04/2026

Whosoever therefore shall humble himself as this little child(ren), the same is greatest in the kingdom of heaven.
(Gospel of Matthew 18:4)

15/04/2026

ABINCIN YININ ECWA
ALHAMIS, 16 GA AFRILU 2026
NASSI: MAHUKUNTA 11:23-28
KAN MAGANA: BARI UBANGIJI YA YANKE HUKUNCI

MAHUKUNTA 11:23-28

23:To, ai, ka ga Ubangiji Allah na Isra'ila ne ya kori Amoriyawa saboda jama'ar Isra'ila. To, yanzu so kake ka ƙwace mana?

24:Kai ba za ka mallaki abin da Kemosh, allahnka, ya ba ka mallaka ba? Dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya mallakar mana, za mu mallake shi.

25:Kana zaton ka fi Balak, ɗan Ziffor, Sarkin Mowab? Ka ji ya taɓa hamayya da Isra'ilawa? Ko kuwa ka ji ya taɓa yin yaƙi da su?

26:Shekara ɗari uku Isra'ilawa s**a yi zamansu a Heshbon da ƙauyukanta, da Arower da ƙauyukanta, da dukan biranen da suke a gefen Kogin Arnon, me ya sa ba ka ƙwace su tun a wancan lokaci ba?

27:Don haka ni ban yi maka laifi ba, kai ne kake yi mini laifi da kake yaƙi da ni. Ubangiji ne alƙali yau, zai shara'anta tsakanin Isra'ilawa da Ammonawa.”

28:Amma Sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika masa ba.

BARI UBANGIJI YA YANKE HUKUNCI

Yefta ya zama shugaba a lokaci mai wuya a Isra'ila, inda zunubi ya cigaba da kawo wahala mai zagayawa.

Ya tsara yakin a matsayin hamayya tsakanin Ubangiji da Kemosh, gunkin Amoriyawa, ya kuma ce mallakar da Isra'ila ta yi wa kasar halal ne tun da Allah ne ya ba su (aya 23).

Ya kalubalanci Amoriyawa su kiyaye abinda Kemosh ya ba su yayin da Isra'ilawa ke kiyaye abinda Ubangiji ya tanada masu (aya 24).

Yafet ya dogara ga Ubangiji don nasara, misalin da za mu iya bi a irin namu kalubalen.

TAMBAYA:
Shin za ka bari Allah ya dauki nauyin rayuwar ka?

ADDU'A:
Auna rayuwar ka da kalubalenka iri-iri. Ka kawo su ga Allah kuma ka bari ya yi maka jagora, cikin sunan Yesu. Amin.

Address

Behind Channel 7, Anglo-Jos
Anglo Jos

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ECWA Church Anglo-Jos, Plateau State posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share