Sheikh Muhd Auwal - albani ZARIA

Sheikh Muhd Auwal - albani ZARIA islamic lacturer and imam of masq.

05/05/2014

Jami’an Gwamnatin kasar Girka sun bada rahoton cewa wasu kananan jiragen ruwan fito biyu dake dauke da dimbin masu kaura sun yi hatsarin kifewa a tsibirin Samos, mutane biyu ne s**a halaka.

26/04/2014

SHEIKH IBRAHIM DISINA YA RUBUTA :
SUNNA TV TA DAWO A KARAMAR RECEIVER !!!!!
A yau da Misalin karfe Biyu na rana ne Sunna Tv ta dawo aiki Bayan tsayawa na Sati Biyu zuwa Uku!!!
Alhamdulillah, Mai kowace Irin Receiver zai iya k**a Sunna Tv a yanzu, Karama ce ko Babba!!!
Babu abinda muka canza na tsarin Shirye shiryenmu, Komai yana nan a gurbinsa!!!! Yau akwai karatun Minhajussunnah!!!!
Ba za a iya k**amu a gurbinmu na da ba, Amma babu wani abinda masu kallo za su canza ko saya !!
Ka mika wannan wannan Adireshi ga mai aikin Setlitedinka, ka ce masa ya laluma maka SUNNA TV a wannan Adreshi k**ar Haka:
FREQUENCY: 12015
SR: 29950 POLARISATION: VERTICAL
SATELLITE : SIRUS 5 DEGRES EST
GUDUMMAWARKA ITACE: KA YI SHARE DIN WANNAN STATUS, SANNAN KA KWAFI WANNAN ADIRESHI KA TURAWA MUTANE A WAYOYINSU. YAWAN HIDIMARKA WAJEN YADA ALKAIRI YAWAN LADANKA A WAJEN ALLAH!!!
A SHA MADARAR SUNNA LAFIYA !!!!!

Alsheikh Muhammad Auwal albani kenan tareda alsheikh Abubakar Umar khandahar
26/04/2014

Alsheikh Muhammad Auwal albani kenan tareda alsheikh Abubakar Umar khandahar

LABARI: Kotu Ta Hana Belin Malamin Jami'ar Jihar KogiBabbar Kotun Tarayya dake Abuja, a zaman da tayi a yau, ta ki aminc...
07/03/2014

LABARI: Kotu Ta Hana Belin Malamin Jami'ar Jihar Kogi

Babbar Kotun Tarayya dake Abuja, a zaman da tayi a yau, ta ki amincewa da bada belin malamin Jami'ar Jihar Kogin nan Dr. Muhammad Nazeef Yunus.

Malam Nazeef ya gurfana a gaban kotun ne sak**akon zarginsa da hannu cikin ta'addacin da kungiyar Boko Haram ta ke yi a kasar nan.

Haka kuma kotun ta hana belin wani dan kasuwa Alhaji Salami Abdullahi da Umar Musa wadanda aka gurfanar da su gaban kotun tare da malamin jami'ar.

Alkalin kotun mai shari'a Gabriel Kolawole ya ce kotun ta ki amincewa da bada belin mutanen da ake zargin ne, saboda kar sanadiyyar hakan, ya kara haifar da karuwar hare-haren Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas.

Mai shari'a Kolawole ya kuma yi Allah-wadai da harin da kungiyar ta kai na baya-bayan nan kan daliban makarantar Kwalejin Gwamnatin Tarayya, dake Buni-Yadi, jihar Yobe.

K**ar yadda alkalin ya bayyana ya ce matakin da kotun ta dauka, ya biyo bayan yanayin da ake ciki a kasar nan makonni hudu da s**a gabata, inda ya kara da cewa ci gaba da tsare wadanda ake zargin zai taimaka wajen samun daidaituwar tsaro a jihohin da abin yake shafa.

Alhaji Salami Abdullahi, daya daga cikin wadanda ake zargin ya nemi kotun da bada belinsa ne sak**akon rashin lafiya da yake fama da ita, sai dai mai shari'a Kolawole ya ce idan don maganar rashin lafiya ne za a ci gaba da duba lafiyar ta sa a karamin asibitin dake cikin kurkukun Koje inda ake tsare da su.

Za a ci gaba da sauraren karar ranar 18 ga watan nan na Maris.

LABARI: SSS Sun K**a Mutane Bakwai Da Ake Zargi Da Hannu Cikin Kashe Sheikh AlbaniHukumar jami'an tsaron farin kaya, SSS...
04/03/2014

LABARI: SSS Sun K**a Mutane Bakwai Da Ake Zargi Da Hannu Cikin Kashe Sheikh Albani

Hukumar jami'an tsaron farin kaya, SSS, ta ce ta k**a wasu mutane su bakwai, ciki har da kwamandan kungiyar Boko Haram da ake zargi da hannu cikin kashe malamin addinin Musuluncin nan, Sheikh Muhammad Auwal Albani Zaria.

Mai magana da yawun hukumar ta SSS, Marilyn Ogar ce ta bayyana hakan, ga manema labarai a yau a harabar babban ofishin hukumar dake Abuja.

'Yan bindigar sun harbe Sheikh Albani ne a ranar 1 ga Fabrairun da ya gabata tare da mai dakinsa da kuma dansa, a hanyarsu ta komawa gida daga inda yake ba wa dalibai karatu.

Mrs. Ogar ta bayyana sunayen wadanda ake zargi da kashe Albanin k**ar haka: Yakub Abdullahi mai shekaru 42, wanda ta ce shi ne kwamandan 'yan Boko Haram na yankin jihohin Kaduna da Neja. Sai Yasir Salihu mai shekaru 35, Ibrahim Shuaibu mai shekaru 22 da Bilyaminu Usman, mai shekaru 22

Sauran su ne: Sahabi Ismail mai shekaru 27; Umar Ismail mai shekaru 35; Musa Abubakar mai shekaru 54.

A kwanan nan jagoran kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau, ya fitar da wata sanarwa, inda ya bayyana cewa su ne s**a kashe malamin

RAHOTO DAGA JARIDAR RARIYA: Cikakken Rahoto Kan Yadda Aka Kashe Sheikh Auwal Albani ZariyaDaga Ibrahim Ammani, Kaduna“Mu...
09/02/2014

RAHOTO DAGA JARIDAR RARIYA: Cikakken Rahoto Kan Yadda Aka Kashe Sheikh Auwal Albani Zariya

Daga Ibrahim Ammani, Kaduna

“Mu duba dai ga sarakunanmu, wadanda sunka rike kasarmu, yau ina su Shehu Mujaddadinmu, mu sani ba zamu dawwama ba.”

Wannan wani baiti ne daga cikin baitoci na wakar Infiraji, wanda dattijon nan marigayi Malam Aliyu Namangi Zariya ya rera a zamanin rayuwar shi.

Kuma wannan waka ta Infiraji daya ce daga cikin wakokin da sanannen malamin nan, mazaunin unguwar Mucciya dake sabon garin Zariya, ke yawan bada misalai da ita, a mafi yawancin wa’azuzzuka da yake gabatarwa a majalisi daban daban, wato Abu Abdurrahman, Muhammad Auwal Adam Albani Zariya.

A karshen makon daya gabata ne wasu ‘yan Bindiga, da ba’a san ko su wane ne ba, s**a yi kwanton bauna s**a harbe shi tare da matarsa da daya daga cikin ‘ya’yansa, a lokacin da yake kokarin shiga gidansa, jim kadan bayan dawowarsa daga bada karatu, wanda ya saba yi a masallacin Juma’a na Salafiyya dake titin Maje Sabon Garin Zariya.

Ga dukkanin mutumin da ya san Auwal Albani, ya san shi a matsayin wani mutum mai jajircewa da kokarin fadin gaskiya komai dacinta, sannan a hannun guda, Albani mutum ne mai tsanani ga dukkanin wani wanda s**a saba da shi ta bangaren akida.

Auwal Adam, ya samo lakabin sunanshi na Albani ne, daga wajen fitaccen malamin nan, mazaunin Saudiyya, marigayi Alsheik Nasirudeenil Albani, wanda ya rasu wasu shekaru da s**a gabata.

Albani ya yi fice, wajen bada fatawowi sababbi wadanda ake ganin cewar sun saba da mazhabar da jama’a s**a gada iyaye da kakanni a tarayyar Nijeriya, wato mazhabar Malikiyya. Wasu daga cikin fatawowin da malamin ya bayar sun hada da halarcin gabatar da sallar Juma’a da sanyin safiya, sannan da wajabcin cin naman doki, da kuma mas’alar saki uku ga mace a lafazi guda, cewa yana matsayin saki guda ne, da saurana mas’aloli da ake wa kallon baki ne a addini.

Adam Albani ya sha amsa gayyata zuwa fadar Mai Martaba Sarkin Zazzau, domin amsa tambayoyi daga bakunan malaman Zazzau, bisa kan wadannan fatawowi da yake bayarwa.

Lokacin da sunan kungiyar nan ya bayyana a Nijeriya, wato Boko Haram a shekarar 2009, karkashin jagorancin Muhammad Yusuf, Albani ya kasance a sahun gaba, wajen caccakar wannan akida, da kuma s**an lamirin shugabanta Muhammad Yusuf, wanda ya bayyana a matsayin wanda ya sani ciki da bai.

Albani ya amsa gayyata daga gwamnati akan wasu kalamai da ya furta wadanda ake ganin suna da nasaba, da taba sha’anin tsaro har sau biyu, kafin daga bisani kotu ta wanke shi, ya dawo ya ci gaba da ayyukan shi k**ar yadda ya saba.

A mafi yawancin lokuta Albani, na nesantar da kanshi daga dukkanin wata kungiya ta addini, inda yake bayyana kanshi a matsayin mai bin tafarkin magabata kawai, (SALAFIYYA) lamarin da ya bambanta shi da sauran takwarorinsa malamai masu da’awar Sunnah a tarayyar Nijeriya. Auwal Albani ya yi fice wajen s**an lamirin shugaban mabiya mazhabin Shi’ah a tarayyar Nijeriya,wato Alsheik Ibrahim Yakub El-Zakzaky, abinda masu nazari ke ganin cewar ba shi yiyuwa, tarihin daya daga cikinsu ya cika, ba tare da an ambato sunan dayan ba, wanda ba ya rasa nasaba, da kasanacewarsu manyan malamai na akidu biyu na musulunci, Sunnah da Shi’ah da ke zaune a gari guda.

Lokacin da wasu ‘yan bindiga s**a harbe, sanannen malamin nan mazaunin birnin Kano, Shiek Ja’afar Mahmud Adam, a shekarar 2007, Adam Albani ya kasance wanda ya fi kowa nuna takaici da damuwarsa akan wannan kisan gilla da aka yi, wanda hakan ta kai shi da shirya wata gagarumar Muhadara a shekarar 2009, mai taken “Waye ya kashe Malam Ja’afar?” Bayan kammala wannan muhadarar ne, malamin ya bayyana yadda ya yi ta samun sakwanni ta waya masu barazana ga rayuwar shi da ta iyalanshi a lokuta daban daban.

Sai dai tambayar da jama’a ke bukatar sanin amsarta ita ce, shin su waye ke da alhakin kaiwa malaman addinin musulunci hari akai akai haka? Bayan kisan da aka yi wa Malam Ja’afar a Kano, an yi nasarar hallaka Malam Muhammadu Dan Mai Shiyya, a garin Sakkwato, sannan sai ga na kwanan nan kisan Malam Albani a Zariya.

K**ar yadda bayanai s**a nuna Albani ya gabatar da wata Muhadara mai taken,”Ina Gaskiya Take Tsakanin Kur’ani Da Bible?” a ranar Juma’ar da ta gabata wato ranar jajibirin da za’a kashe shi wanda wani malami masanin Bilble mai suna Farfesa Dawud ya yi mishi ta’alikinta. Sannan a ranar Asabar a karatun da yake yi na Sahihul Bukhari a masallacin Markazul Salafiyya, malamin ya tsaya akan babin aikin Hajji, hadisi na karshe da ya karanta shine wanda ke bayanin wata mata ta tambayi Annabin Rahama (SAW) ko za ta iya yi wa mahaifinta aikin Hajji bayan rasuwarshi? Sannan malamin ya yi alkawarin gabatar da wata muhadara a ranar Lahadi da misalin karfe takwas na dare, mai taken “In Kun San Wata Ba ku San Wata Ba” muhadarar da bai sami gabatarwa ba kenan aka kashe shi a ranar Asabar da misalin karfe goman dare.

Akwai abin mamaki da ta’ajibi dangane da kisan da aka yi wa Sheik Albani, k**ar yadda wani makwabcin malamin yake bada shaida akan abinda ya ganewa idanuwanshi na abin tashin hankalin da ya faru. Ustaz Umar Ahmad yace sun hango wata mota baka kirar Jeep, tunda misalin 09:30 pm na dare, tana shawagi a kusa da gidan malamin, a daidai lokacin da Malam Albani yake dawowa daidai kwanar kofar gidanshi ne,wadannan makisa su biyar s**a afka wa motarshi da harbi gaba daya, kuma nan take s**a harbe matarshi mai suna Fatima, da danshi Abdullahi, a daidai wannan lokaci ne Malam Albani ya fara kira a gare su da cewar, kada su kashe kowa amma su kashe shi shi kadai, sun ci gaba da harbinsa ta ko’ina a jikinsa, kafin daga bisani s**a fito da shi daga cikin motar, s**a yi ta harbinsa, har sai da s**a tabbatar baya motsi, sannan s**a koma da gudu cikin motar tasu s**a gudu.

Bayan an kai shi asibiti ne ya cika sak**akon munanan raunukan da ya samu musanma a kan shi, wanda aka tabbatar da cewar an sami hujin harsasai sama da bakwai a kokon kan na shi.

Hankalin jama’a ya tashi matuka a lokacin da aka fito da gawar marigayin domin gudanar mata da sallar janaza, sak**akon yadda jini ya bata likkafinin malamin, a haka a gudanar masa da sallah shida iyalin tashi da kuma dan shi, kafin daga bisani aka binne su a makabarta.

Da yake bayyana yadda ya kalli wannan kisan gilla da aka yi, sanannen malamin addinin Islama mazaunin garin Jos,Alsheik Alhassan Sa’idu Jos, yace wannan kisan gilla da ake yi wa malaman addinin Islama, alama ce dake nuna cewar da akwai wata kullalliya daga karkashin kasa, da ake da ita na kawar da dukkanin wani malami mai fadin gaskiya a doron kasa, ya bada misali da kisan da aka yi wa Malam Ja’afar Adam, amma abin bakin ciki sak**akon rashin daukar matakin da ya dace, ya haifar da sake kai wani hari mak**ancinsa, indan kuma har ba’a gaggauta daukar matakiba, to abin zai ci gaba ne in ji malamin.
Shi ma da yake bayyana ra’ayinsa dangane da wannan jafa’i da ya faru, Alsheik Tukur Adam Almannar, yace wannan kisa da ake yi wa malaman musulunci a arewacin kasar, yana k**a da wani Bom da aka dasa a cikin al’umma da niyyar tarwatsa su, ta inda za’a kai ga wani matsayin da jama’a za su rasa jagora a addinan ce, wanda zai iya sa su a hanya madaidaiciya. Daganan sai ya yi kira ga gwamnati da ta gaggauta daukar matakin binciko gami da kamo wadanda ke da hannu a cikin wannan aika aika domin hukunta su.

Rana daya bayan rasuwar Malam Albani tare da matarshi da dan shi guda, shi ma daya dan na shi mai suna Abdul Bari, ya rasu a washe gari sak**akon raunukan da ya samu a yayin harin, yayin da dayan dan na shi mai suna Abdul Hakk ke ci gaba da karbar magani a Asibiti.

Dubban jama’a ne daga sassa daban daban s**a halarci jana’izar tashi, wanda aka yi a gidansa dake Mucciya sabon garin Zariya, malamai da dama ne daga ciki da wajen kasar, s**a hallarci jana’izar, da dama daga cikinsu, sun kasa cewa komai sak**akon hawaye dake ta zuba a idanuwansu.

An haifi Malam Muhammad Auwal Albani a unguwar Mucciya dake yankin karamar hukumar Sabon Gari, a shekarar 1960, yayi karatunsa na Firamare a unguwar tasu, kafin daga bisani ya wuce kwalejin Barewa dake Zariya, sannan ya yi karatun digirin shi a jami’ar Ahmadu Bello Zariya, ya rasu ya bar mata biyu da ‘ya’ya da dama.

SU WAYE S**A KASHE ALBANI ZARIYA. - Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud GumiA cikin karatun da ya gabatar a ranar Lahadi da...
07/02/2014

SU WAYE S**A KASHE ALBANI ZARIYA. - Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi

A cikin karatun da ya gabatar a ranar Lahadi da ta gabata 2/2/2014 ranar da aka yi jana'izar Sheikh Muhammad Auwal Adam Albanin Zariya malam ya yi bayanin asalin fitinar kisan musulmi.

Tun daga lokacin Khalifa Uthmanu Bin Affan da yadda Manzon Allah SAW ya fada masa cewar akwai wata tufa da za a saka maka kada ka cire ta sai mun hadu da kai a aljannah. Da yadda wadancan yara s**a kashe Aliyu Bin Abi Dalib.

Sahabbai tun suna da rai s**a fara shaida irin wannan mummunan lamari, kuma s**a yi ittifaki cewar wadannan masu kisa suna manzon Allah ya bayar da Labari.

"Yan Boko Haram na asali za su iya kashe Albani domin kowane zamani akwai irin wadancan yara da manzon Allah ya bada labarinsu"

"To amma kuma akwai wadansu da za su iya fakewa da sunan boko haram domin su cimma bukatunsu"

Akwai wata daula wacce ta ke yin irin wadannan miyagun aiki wanda sardauna na shugabantar al'ummarsa bai san da ita ba, haka Murtala da Abacha duk wadannan dauloli su ne s**a kashe su. Saboda haka imma dai Boko Haram ta kashe Sheikh Auwal Albani ko kuma "Kwamando" wadanda suke cikin hukuma.

Domin sauraron cikakken wannan karatu za ku iya saukar da shi ta wannan hanya http://dandalinsunnah.com/multimedia/AhmadGumi/siyasa41.mp3

Muna rokon Allah Madaukakin sarki ya gafartawa Sheikh Auwal Albani da sauran Malamai da s**a riga mu gidan gaskiya.

====
Kada a manta da yada wannan karatu ta duk wata hanya da za ku iya mun gode - TEAM
====

07/02/2014

ALLAHU AKBAR!!!
_____________________
Wadan nan sune ZARATAN KOMANDODI da s**a gaji Malamin mu SHEIKH AUWAL ALBANI ZARI ga sunan su k**ar haka:- 1, MALAM MUSA SAHABI
2. MALAM AUWAL MAI SHAGO
3. MALAM ASGAR
4. MALAM MUSA MINSHAWY 5. MALAM UMAR
6. MALAM DAUDA AZZHAHIRI
SUNNAH NO GOING BACK INSHA ALLAH!!!
_________________________
Ya Allah ka kare mana su da duk wani sharrin mai sharri da duk hasadar mai hasada... Allahumma Ameen

Allahu AkbarA yau ne Dr. Ibrahim Jalo Jalingo( Shugaban majalisar malaimai na kasa) ya jagoranci sallar juma'a a sa'abon...
07/02/2014

Allahu Akbar

A yau ne Dr. Ibrahim Jalo Jalingo( Shugaban majalisar malaimai na kasa) ya jagoranci sallar juma'a a sa'abon masallacin mu na Taseer Foundation a Jos........

Allah ya saka da alkairi Dr

صلى الله عليك وسلم يا سيدي يا رسول الله
07/02/2014

صلى الله عليك وسلم يا سيدي يا رسول الله

ALLAHU AKBAR.....ALLAH YAYIWA MALAM RAHAMA.
07/02/2014

ALLAHU AKBAR.....ALLAH YAYIWA MALAM RAHAMA.

Daga: Abu-Ameena Abdullahi Hamisu ALLAHU AKBAR! WAYANNAN KALAMAN ASH-SHEIKH ALBANI ZARIA NE GA DANDAZON JAMA'A A KOFAR F...
07/02/2014

Daga: Abu-Ameena Abdullahi Hamisu

ALLAHU AKBAR! WAYANNAN KALAMAN ASH-SHEIKH ALBANI ZARIA NE GA DANDAZON JAMA'A A KOFAR FADAR SARKIN ZAZZAU ASA'ILIN DA MASARAUTAR ZAZZAU TA GAYYACE SHI TARO TACI MISHI MUTUNCI AKAN ALLURAR POLIO DA KUMA RAYA SUNNAR SALLAR JUMA'A KAFIN RANA TAYI ZAWALI DA 'DALIBANSHI S**A GABATAR.

Ash-sheikh Albani Zaria ya fara bayani ne da hudubatul ha'ja sannan daga bisani ya fara bayani k**ar haka;

"Jama'a yan uwana musulmi kowa ya natsu mu dauko salsalar abun da ya faru. Sanannan abune kowa ya sani bama riko da mazhaba kwara daya a manhajin da muke tafiya akai. Ma'ana a inda mazhaba ta dace da sunnah muna tare da ita, a inda kuma takauce bama tare da ita. Akarkashin wannan da kuma hadisan Annabi (SAW) yasa muke gabatar da sallolin jumuar mu a lokuta mabanbanta, domin ita sallar jumua bata da tak**amman lokaci kwara daya. Ma'ana a wasu lokuta manzon Allah (SAW) yana yin sallar jumu'a da hantsi, wasu lokuta da tsakiyar rana ko mak**ancin haka.

Amma Gaskiyar abun dake faruwa shine; andai fake da sallar juma'a ne kawai akeso a yake mu. Ma'ana; Rigima ne wasu suke so su samar a 'kasar zazzau saboda dalilan su na siyasa da kuma samun kudi da tsaro.

Alhamdulillah, na halarci wannan taro kuma na gabatar musu da ingantattun hadisai da asarai da s**a tabbatar da cewa za'a iya yin sallar jumua kafin rana tayi zawali. Amma abun takaici shine wasu malamai a fadar sunce su basu amince da sallar juma'a kafin rana tayi zawali ba saboda jamhur basu yadda da ita ba.

Jama'a! matsalar da aka samu shine, ni Albani tun da nayi magana so daya ba a kara bani dama na'yi wata magana ba. Innayi yunkuri zan yi magana sai ace ba jayayya akeso ayi ba, kuma ga littattafai akalla na'zo dasu guda takwas amma ba'a bari na karantasu ba. Amma muna addua Allah ya shiryar da wayannan malaman

Daga karshe, Sarkin zazzau Dr Shehu Idris yace bai yarda da irin wannan sallar jumuar da muka yi ba kuma ya hana. Ni kuma Albani nace mishi mu mun yarda da ita domin manzon Allah yayi umarni kuma sahabbai sun yi.
Sarkin zazzau ya tabbatar min da cewa zasu yi amfani da jamian tsaro .To amma jama'a kunsan dalilin da yasa s**a ce zasu shigo da jamian tsaro? *A'a*! So suke muyi tashin hankali saboda suna so su zamar da zaria ta zama maiduguri domin su cimma manufofin su na siyasa.

Saboda haka, tashin hankali baza ayi ba, jamian tsaro baza kusha jinin musulmi ba, tashin hankali bai kafa kasar zazzau ba kuma mu yayan zagezagi baza muyi tashin hankali ba. Amma za mu zauna lafiya, za ayi karatu kuma za ayi aiki da sunnah. Jama'a ku kwantar da hankalinku, kada wanda ya tayar da hankalinshi, kada ku zagi kowa, kada kuyi hayaniya da kowa, amma zaman lafiyar da basu so wallahi shi za'ayi.

An zalumcemu an hana mu magana. Amma tunda ga taron yan jaridu, to ku isar da wannan sakon ga dukkannin duniya;
Na farko muna kira ga malaman Sarki da mak**antansu dasu fito suzo gaban sarkin zazzau su zauna da yan tijjaniyya su tuhumcesu a ina s**a samo maulidin zagaye k**ar yadda s**a tuhumcemu akan sallar jumua kafin rana tayi zawali. Sannan muna kara kira gasu wayannan mallaman dasu zo da yan shia su tuhumcesu akan zagin Umar, Abubakar, usman, Aisha da Hafsat a gaban sarkin zazzau k**ar yadda s**a yi mana.

Sarkin Zazzau Allah ya yafe maka tunda mun gano anason ayi amfani dakai ne a kashe yayan zagezagi, to jami'an tsaro baza kusha jinin mutanen zazzau ba.

Don haka jama'a kowa yaje ya zauna lafiya, zamu sanar daku lokacin daza a cigaba da sallar jumua insha'Allahu. Subhanakallahumma Wabi hamdika Ash-hadu anla'ilaha-illaanta astagfiruka wa'atubu ilaik.

Address

New Cairo
Cairo

Opening Hours

Monday 2pm - 2am
Tuesday 2pm - 2am
Wednesday 2pm - 2am
Thursday 2pm - 2am
Friday 2pm - 2am
Saturday 2pm - 2am
Sunday 2pm - 2am

Telephone

+201113357391

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sheikh Muhd Auwal - albani ZARIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share